daga Mukhtar Khalil
Rahotanni sun bayyana cewarma’aikatar aikin hajji da Umara ta kasar ce ta bayyana hakan cikin wata sanarwa da ta fitar ,wadda ta bayyana sharudda da za’ai amfani da su yayin ibadar.
Sanarwar tace hukumar ta amince mutane miliyan daya daga ciki da wajen Kasar su gudanar da aikin hajjin, Amma bisa sharadin bin matakan kare kai daga annubar Covid-19, wadda ita ta hana gudanar da ibadar a Shekarun 2020 da 2021.
Daga cikin sharuɗɗan ma’aikatar ta ce bazata bari dattawan da suka haura Shekaru 65 a duniya su gudanar da ibadar ba a bana, Sannan suka ce duk wanda zai shiga Kasar sai an yi masa gwajin Corona na aƙalla kwana biyu kafin ya shiga kasar ta Saudiyya.
Sanarwa ta kara da cewa dole ne duk maniyata aikin hajji bana sai an yi musu allurar rigakafin Covid-19 wadda kasar Saudiyya ta amince da ita, da kuma bin sauran matakan kula da Lafiya kamar yadda aka saba.
Idan ba a mantaba Kadaura24 ta rawaito Shekaru biyu kenan annubar Covid-19 tana hana gudanar da aikin hajji da mutane Masu yawa a duniya.

Murtala Sule Garo yafi kowa Cancantar Zama Mataimakin Gwamnan Kano.
Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta sanar da rufe karɓar biyan kuɗin Hajji na shekarar 2026.
TARON KOYAR DA KIWON KAJI DA KIFI: KPA
Dalung yayi Alhinin halin da Nigeria ke Ciki .
Manoma sun Kira ga Gwamnati Tarayya tayi taka Tsan-Tsan
Gwamna Peter Mbah na Enugu ya koma jam’iyyar APC
Group demands full implementation of Katsina PWDs discrimination law
Jigawa to Provide Three Daily Meals for Pilgrims in 2026 Haj
Kano Police, NEMA Strengthen Partnership on Disaster Response
Kano Police Arrest Two Over ‘Aljannu’ Phone Scam, Recover 28 SIM Cards
Federal University of Education, Zaria Matriculates Over 5,000 Pioneer Students
AGILE Project Drives Education Transformation in Jigawa State