Ƙungiyar ‘Yan Jarida ta NUJ a jihar Adamawa na fafutukar ganin an hukunta wani mutum tsohon ma’akacin hukumar wutan lantarki ta Najeriya ta PHCN mai suna Malam Ibrahim Aliyu wanda ake zargin yayi wa tsohowar matarsa, Nafisa Vandi dukan kawo wuƙa.
A sanarwar da shugaban ƙungiyar ‘yan jarida a reshen jihar Adamawa, Ishaka D. Dedan ya fitar a jiya Laraba, ya shaida cewa Nafisa Vandi ‘yar jarida ce da ke aiki da kafar yaɗa labarai ta ABC , yace tsohon mijinta wanda korarren ma’akacin PHCN ne yayi mata ɗan karen duka wanda yayi sanadiyar ji mata ciwo don haka suke neman a bi mata haƙkinta a hukunta wanda ake zargin.
Sanarwar ta ce duk da dai ‘yan sanda sun kama wanda ake zargin, ƙungiyar na fatan ayi masa hukuncin cikin lokaci inda ta neme sauran ƙungiyoyin kare hakkin mata na duniya da su shiga lamarin.

Murtala Sule Garo yafi kowa Cancantar Zama Mataimakin Gwamnan Kano.
Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta sanar da rufe karɓar biyan kuɗin Hajji na shekarar 2026.
TARON KOYAR DA KIWON KAJI DA KIFI: KPA
Dalung yayi Alhinin halin da Nigeria ke Ciki .
Manoma sun Kira ga Gwamnati Tarayya tayi taka Tsan-Tsan
Gwamna Peter Mbah na Enugu ya koma jam’iyyar APC
CP Bello Inspects Police Constables Screening Exercise in Gusau
Police Repel Bandit Attacks in Maru, Bukkuyum LGAs of Zamfara
NUJ Kebbi Condoles Gov Idris K/HA Members, Zuru Emirate On The Passing Of Speaker MUHAMMAD USMAN ZURU
Police Arrest Motorcycle Theft Suspect, Recover Stolen Bajaj Boxer in Kano
Catholic Diocese Calls on Federal, Kebbi Govts To Restore Security in Shanga