Menu

JAMOH YA JAJANTAWA EL-RUFAI KAN HARIN DA AKA KAI KADUNA.

Admin 4 years ago

Dakta Bashir Jamoh ya jajanta wa gwamnatin jihar Kaduna kan hare-haren da suka hada da titin jirgin kasa daga Abuja zuwa Kaduna da kuma mamaye filin jirgin sama na Kaduna wanda ya yi sanadin mutuwa da jikkata da kuma sace fasinjoji da ba a tantance adadinsu ba.

A wata wasika da ya aikewa Gwamna Nasir El-Rufai na jihar Kaduna, Jamoh, wanda kuma shi ne Darakta Janar na Hukumar Kula da Jiragen Ruwa ta Najeriya NIMASA, ya bayyana kaduwarsa da faruwar lamarin, yayin da ya mika ta’aziyyarsa ga iyalan wadanda suka rasu da daukacin mutanen jihar Kaduna.

Allah (SWT) na nan tare da ku a wannan lokaci na alhini, muna kuma rokonSa da Ya samar da zaman lafiya, ci gaba da wadata a jihar Kaduna, in ji Jamoh.

Dokta Jamoh ya bukaci al’ummar Kaduna da su ci gaba da yin imani da Gwamnatin Jiha da ta Tarayya a kokarinsu na ganin an magance matsalolin tsaro da Jihar ke fuskanta.

Ya kara da cewa “Nagarta za ta rinjayi mugunta a koyaushe. Mu kasance masu lura a matsayinmu na ‘yan kasa nagari tare da sanar da jami’an tsaro da abin ya shafa abubuwan da suka shafi shakku ko abin da ba a gane masa a cikin jihar da kewaye.”