Menu

MINISTAN SUFURI YA BUKACI HUKUMAR NIMASA DA TA SAMAR DA TASHAR KERAWA DA GYARA JIRAGEN RUWA

Admin 4 years ago

Ministan harkokin sufuri, Alhaji Mu’azu Jaji Sambo ya bukaci hukumar kula da harkokin iyakokin ruwan kasar nan da ta samar da tashar kerawa da kuma gyaran jiragen ruwa.

Shugaban hukumar, Dr Bashir Yusuf Jamoh ne ya bayyana haka a wata sanarwa da mataimakin darakta a sashin hulda da jama’a na hukumar, Mr Edward Osagie ya rabawa manema labarai a birnin Ikko.

Dr Bashir Yusuf Jamoh ya ce Ministan ya bayyana fatan cewa nan da watanni kadan masu zuwa, hukumar za ta samar da wannan tasha don amfanin jama’ar kasar nan.

Ya kara da cewa hukumar na aiki ba dare ba rana wajen aiwatar da umarnin Ministan ta hanyar yin hadin gwiwa tare da hukumar kula da tashoshin jiragen ruwan kasar nan wato NPA.

Shugaban hukumar ta NIMASA yace hukumar ta kammala tattaunawa da hukumar NPA da sauran masu ruwa da tsaki kan yanda za a kaddamar da tashar inda zata dinga aiki a wani bangare na hukumar ta NPA.