Rundunar yan sanda ta Jihar Kano ta ce ta kama wani gungun masu ƙwacen waya su 6 da su ke addabar al’umma a jihar.
Kakakin rundunar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa ne ya baiyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a yau Lahadi.
Ya ce an yi kamen ne bisa umarnin Sifeto-Janar na Ƴan Sanda kan cewa a tsaftace Kano daga duk wani aikin ɓatagari, musamman ƴan daba, ƴan ƙwaya da sauran laifuka, musamman a yayin bukukuwan Kirsimeti.
Kiyawa ya ce a na cikin sintirin ne a ka cafke waɗannan masu ƙwacen wayar su 6.
Ya ƙara da cewa an samu babura masu ƙafa uku da wayoyi 17 da su ka ƙwacewa mutane.
Kiyawa ya yi bayanin cewa masu laifin su na basaja ne a zuwan su matuƙa babur mai ƙafa uku ne sai su riƙa ƙwacewa fasinjoji wayoyin salula.
Ya ƙara da cewa idan an gama bincike, za ai kai su kotu domin su girbe abinda su ka shuka

Yusuf Clears N32bn Gratuities, Death Benefits Backlog in Kano
New Test Post 1
test34
test
Kano Police Roll Out Activities for National Police Day 2026
TEF to Announce 2026 Entrepreneurship Programme Cohort March 22
CP Bello Inspects Police Constables Screening Exercise in Gusau
Police Repel Bandit Attacks in Maru, Bukkuyum LGAs of Zamfara
NUJ Kebbi Condoles Gov Idris K/HA Members, Zuru Emirate On The Passing Of Speaker MUHAMMAD USMAN ZURU
Police Arrest Motorcycle Theft Suspect, Recover Stolen Bajaj Boxer in Kano
Catholic Diocese Calls on Federal, Kebbi Govts To Restore Security in Shanga