A cewar hukumar ta NCDC, sabbin mutum 859 suka kamu da cutar a ranar Litinin da ta gabata.WASHINGTON D.C. —
Hukumar da ke yaki da yaduwar cututtuka ta NCDC a Najeriya ta ce mutum 3, 024 cutar coronavirus ta kashe tun daga lokacin da annobar ta barke zuwa yanzu.
NCDC ta bayyana hakan ne a kididdgar da ta fitar a ranar Litinin wacce ta bayyana iya adadin sabbin mutanen da aka gano suna dauke da cutar a ranar 27 ga watan Disambar 2021.
A cewar hukumar, sabbin mutum 859 suka kamu da cutar a ranar ta Litinin.
Daga cikin wannan adadi mutum 555 a jihar Legas aka same su, 57 a babban birnin tarayya na Abuja sai jihar Rivers mai mutum 44.
Sauran jihohin sun hada da Filato mai mutum 43 sai Edo mutum daya da Ondo mai mutum 34.
Kwara na da mutum 23 Kano 18, Ogun 16, Enugu 11, Oyo 6, Delta 5, Bauchi 3 sai Bayelsa mai mutum 3 ita ma.
Hukumar ta NCDC ta ce jimullar mutanen da aka gano cutar ta harba a kasar baki daya ta tsaya a dubu 238, 420 ya zuwa ranar Litinin.
voa Hausa


Yusuf Clears N32bn Gratuities, Death Benefits Backlog in Kano
New Test Post 1
test34
test
Kano Police Roll Out Activities for National Police Day 2026
TEF to Announce 2026 Entrepreneurship Programme Cohort March 22
CP Bello Inspects Police Constables Screening Exercise in Gusau
Police Repel Bandit Attacks in Maru, Bukkuyum LGAs of Zamfara
NUJ Kebbi Condoles Gov Idris K/HA Members, Zuru Emirate On The Passing Of Speaker MUHAMMAD USMAN ZURU
Police Arrest Motorcycle Theft Suspect, Recover Stolen Bajaj Boxer in Kano
Catholic Diocese Calls on Federal, Kebbi Govts To Restore Security in Shanga