Menu

A Guji Zuba Shara A Magudanan Ruwa don Kaucewa Ambaliyar Ruwa -Ibrahim Dan’azumi Gwarzo

Admin 4 years ago

Daga Sani Danbala Gwarzo

Anyi kira ga daukacin alumar jahar kano dasu guji cushe magudanar ruwa,Dan kauceawa yawaitar ambaliyar ruwa,Kiran dai ya fito ne daga sabon kwamishinan kasafi da tsare tsare na jahar kano,Alhaji Ibrahim Dan, azumi gwarzo yayin ganawa da manema labarai a ofishinsa

Kwamishinan yace gwamnatin jihar kano karkashin jagorancin gwamna Abdullahi ganduje na Iya kokari wajen samar da aiyukan cigaba ga aluma,

sannan Dan azumi gwarzo ya jajantawa daukacin Yan kasuwar da iftilain ambaliyar ruwan ya shafa da Kuma Mika taaziya ga iyalan wadanda suka rasu a rushewar ginin Nan Mai hawa biyu na kasuwar Yan waya dake Kan titin Beirut.