Usman Ahmed, kaduna
Barrister Solomon Dalung, tsohon ministan matasa da wasanni zamanin marigayi Shugaba Muhammadu Buhari, yayi tsokaci a yayin zantawa da yan jarida lokacin gudanar da bikin cika shekaru ashirin da biyar da kafuwar kungiyar Dattawan Arewa.
A fadinsa, tsohon ministan yace kamata yayi ace Kuka a keyi da alhini, ba bikiba.
Yace “yaran mu fiye da dari, Mata, yan makaranta na tare da yan bindiga a daji, wadanda aka daukesu karfi da yaji a makarantunsu.
Ya Kara da cewa kamata yayi a yi alhini, ayi dubi, ta duk yadda za’a kubutar da kananan yan makarantar, Wanda basu ji ba, Basu gani ba.
Yace, yanzu haka iliminsu ya zama wani abu, la’akari da halin dasu ke ciki.
Ya Kara da cewa, “yanzu da ace yaranmu na cikinsu, da bama nan, dole muna chan, nemar mafitarsu”.
Ya Kuma ce, ya zama dole a samar musu mafita.
Akarshe ya yabawa kungiyar Dattawan Arewa da nasu kokarin na gudanar da taron, da Kuma Kira ga al’ummar Arewa dasu kula da ilimi, noma da kasuwanci

Murtala Sule Garo yafi kowa Cancantar Zama Mataimakin Gwamnan Kano.
Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta sanar da rufe karɓar biyan kuɗin Hajji na shekarar 2026.
TARON KOYAR DA KIWON KAJI DA KIFI: KPA
Manoma sun Kira ga Gwamnati Tarayya tayi taka Tsan-Tsan
Gwamna Peter Mbah na Enugu ya koma jam’iyyar APC
Governor Yusuf, Emir Sanusi Host Special National Prayer in Kano
Kano, FG Partner to Boost Livestock Development, Food Security
NADCEL 2026: Army Sensitises Kano Students on Discipline, Career Pathways
Tijjaniyya Shura Council Endorses Gov. Yusuf for Second Term
Kano Pillars, seven others qualify for NBBF Super 8 Premier league