Usman Ahmed, kaduna
Barrister Solomon Dalung, tsohon ministan matasa da wasanni zamanin marigayi Shugaba Muhammadu Buhari, yayi tsokaci a yayin zantawa da yan jarida lokacin gudanar da bikin cika shekaru ashirin da biyar da kafuwar kungiyar Dattawan Arewa.
A fadinsa, tsohon ministan yace kamata yayi ace Kuka a keyi da alhini, ba bikiba.
Yace “yaran mu fiye da dari, Mata, yan makaranta na tare da yan bindiga a daji, wadanda aka daukesu karfi da yaji a makarantunsu.
Ya Kara da cewa kamata yayi a yi alhini, ayi dubi, ta duk yadda za’a kubutar da kananan yan makarantar, Wanda basu ji ba, Basu gani ba.
Yace, yanzu haka iliminsu ya zama wani abu, la’akari da halin dasu ke ciki.
Ya Kara da cewa, “yanzu da ace yaranmu na cikinsu, da bama nan, dole muna chan, nemar mafitarsu”.
Ya Kuma ce, ya zama dole a samar musu mafita.
Akarshe ya yabawa kungiyar Dattawan Arewa da nasu kokarin na gudanar da taron, da Kuma Kira ga al’ummar Arewa dasu kula da ilimi, noma da kasuwanci

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta sanar da rufe karɓar biyan kuɗin Hajji na shekarar 2026.
TARON KOYAR DA KIWON KAJI DA KIFI: KPA
Manoma sun Kira ga Gwamnati Tarayya tayi taka Tsan-Tsan
Gwamna Peter Mbah na Enugu ya koma jam’iyyar APC
Gwamna Buni ya naɗa tsohon ɗan majalisar wakilai, Ismail Gadaka a matsayin sabon sarkin Gudi
Ambassador Dr. Amina Umar Namadi: A First Lady Defined by Compassion, Service, and Humanity
Police Rescue Abducted Three-Day-Old Baby, Arrest Two Suspects in Nasarawa
Governor Yusuf Mourns Alhaji Nuhu Dantani
ADC Leaders Reject INEC Decision, Vow to Resist, Mobilise Support in Otukpo
Police Disburse ₦9.26m to Families of Fallen Officers in Kano