Gwamnan Jihar Enugu, Peter Mbah, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP tare da komawa jam’iyyar APC.
Mbah ya bayyana haka ne a ranar Talata yayin wani taron manema labarai da ya gudanar a Enugu, inda ya ce matakin nasa na komawa APC ya biyo bayan burinsa na inganta hidima ga al’ummar jihar da kuma daidaita kansa da hangen nesa na jam’iyyar wajen ci gaba da bunƙasa tattalin arziki.
A cewarsa, shiga jam’iyyar APC zai ba da dama mafi faɗi na haɗin gwiwa da ci gaba da zai taimaka wajen bunƙasa Jihar Enugu.
“Na kuduri aniyar ci gaba da inganta cigaban jiharmu tare da tabbatar da cewa jama’armu suna amfana da mulkin da ya dogara da haɗin kai da ci gaba mai ɗorewa. Tsarin jam’iyyar APC zai ba mu damar cimma waɗannan manufofi,” in ji shi.
Gwamnan ya kuma bayyana godiya ga tsohuwar jam’iyyarsa, PDP, bisa goyon baya da ta ba shi tsawon shekaru, yana mai cewa matakin sauya sheƙa ba abu ne da aka ɗauka da wasa ba.
Asalin Labari…. Daily Nigeria Hausa

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta sanar da rufe karɓar biyan kuɗin Hajji na shekarar 2026.
TARON KOYAR DA KIWON KAJI DA KIFI: KPA
Dalung yayi Alhinin halin da Nigeria ke Ciki .
Manoma sun Kira ga Gwamnati Tarayya tayi taka Tsan-Tsan
Gwamna Buni ya naɗa tsohon ɗan majalisar wakilai, Ismail Gadaka a matsayin sabon sarkin Gudi
Ambassador Dr. Amina Umar Namadi: A First Lady Defined by Compassion, Service, and Humanity
Police Rescue Abducted Three-Day-Old Baby, Arrest Two Suspects in Nasarawa
Governor Yusuf Mourns Alhaji Nuhu Dantani
ADC Leaders Reject INEC Decision, Vow to Resist, Mobilise Support in Otukpo
Police Disburse ₦9.26m to Families of Fallen Officers in Kano