Gwamnan Jihar Enugu, Peter Mbah, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP tare da komawa jam’iyyar APC.
Mbah ya bayyana haka ne a ranar Talata yayin wani taron manema labarai da ya gudanar a Enugu, inda ya ce matakin nasa na komawa APC ya biyo bayan burinsa na inganta hidima ga al’ummar jihar da kuma daidaita kansa da hangen nesa na jam’iyyar wajen ci gaba da bunƙasa tattalin arziki.
A cewarsa, shiga jam’iyyar APC zai ba da dama mafi faɗi na haɗin gwiwa da ci gaba da zai taimaka wajen bunƙasa Jihar Enugu.
“Na kuduri aniyar ci gaba da inganta cigaban jiharmu tare da tabbatar da cewa jama’armu suna amfana da mulkin da ya dogara da haɗin kai da ci gaba mai ɗorewa. Tsarin jam’iyyar APC zai ba mu damar cimma waɗannan manufofi,” in ji shi.
Gwamnan ya kuma bayyana godiya ga tsohuwar jam’iyyarsa, PDP, bisa goyon baya da ta ba shi tsawon shekaru, yana mai cewa matakin sauya sheƙa ba abu ne da aka ɗauka da wasa ba.
Asalin Labari…. Daily Nigeria Hausa

Murtala Sule Garo yafi kowa Cancantar Zama Mataimakin Gwamnan Kano.
Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta sanar da rufe karɓar biyan kuɗin Hajji na shekarar 2026.
TARON KOYAR DA KIWON KAJI DA KIFI: KPA
Dalung yayi Alhinin halin da Nigeria ke Ciki .
Manoma sun Kira ga Gwamnati Tarayya tayi taka Tsan-Tsan
Police Arrest 248 Suspects, Recover Weapons and Drugs in Kano Crackdown
Akwa Ibom Police Command Warns Against Jungle Justice, Praise Doctor’s Heroism
Sen. Mohammed Sani Musa Emerges Consensus Candidate for Niger East as Gov. Bago Resolves APC Dispute
Why Senator Musa Emerged as Consensus Candidate
Governor Yusuf Approves 166 Solar-Powered Boreholes to Ease Water Stress in Kano
Barau Emerges APC Candidate for Kano North, Urges Support for Tinubu, Abba