Kungiyar Cigaban Al’ummar Anguwan Kakaki (KPA), Karkashin jogoran Alh. Amin Mahmood da hadin gwaiwar Asibitin Koyarwa na Dabbobi dake Karkashin Jami’ar Ahmadu Bello dake Zaria ta shirta bita don horar da matasa da Mata na kwana daya Kan dubarun kiwon kaji da Kifi.
Da yake gabatar da makala ta farko a Kan kiwon Kaji Professor Lawal Sa’idu daga Asibitin Koyarwa na kiwon dabbobi na Jami’ar Ahmadu Bello dake Zaria, yayi jawabi Mai tsawo Kan sabbin dubarun kiwon kaji musamman masu Samar da nama, daku yanda zaa rage yawan mutuwar wadannan Kaji lokacin kiwonsu don samun riba Mai yawa.
Shima anasa Jawabin Mai gabatar da kasida ta biyu akan kiwon kifi, Wanda kuma shine Shugaban wannan Kungiyar ta Cigaban Al’ummar Kakaki Alh. Amin Mahmood, ya dauki lokaci ma tsawo don fayyace Yadda zaa dunkari kiwon kifi tsakanin matasa da Mata, da kuma nuna irin alherin da Ake samu cikin wannan kiwo.
Daga bisani yaja hankalin matasa dasu dage wajen gannin sun rungumi wannan taginashi da Uwar Kungiyar Cigaban Al’ummar Kakaki ke bayar lokaci bayan lokaci.
Tunda farko Shugaban Kwamitin dattijan Anguwan Kakaki Alh. Hassan Dalhatu (Cigarin Zazzau), Wanda yasami wakilcin Alh. Jafaru Suleiman ya godewa daukacin shuwagabannin wannan Kungiya ganin Yadda suka dukufa wajen bada tallafi tare da horaswa ga matasa don ganin sun dogara da Kansu.
Itama Shugabar Kungiyar Mata Manoma ta Nigeria reshen karamar hukumar Zaria Hajia Aisha Muhammad ta godewa wannan Kungiya saboda hangen nesanta na shirya wannan horo don ganin Mata da matasa sun tsaya da kafafunsu.
Shugabar tace yadace a Samar da wata hanya da zasu rinka samun irin kifi a saukake don kiwo, da kuma kafa gidauniyar tallafawa juna tsakanin Mata manoma da Kungiyar KPA.
A jawabinsa na godiya maitainakin Shugaban Kungiyar Cigaban Al’ummar Kakaki Alhaji Alhassan Nuhu ya nuna farin ciki mara misaltuwa da murna da irin wadannan bita da Ake kokarin shiryawa don ganin matasan wannan Anguwa sun Zama abin koyi, kana yayi addaur Allah ya maida kowa gida lafiya Amin.

Murtala Sule Garo yafi kowa Cancantar Zama Mataimakin Gwamnan Kano.
Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta sanar da rufe karɓar biyan kuɗin Hajji na shekarar 2026.
Dalung yayi Alhinin halin da Nigeria ke Ciki .
Manoma sun Kira ga Gwamnati Tarayya tayi taka Tsan-Tsan
Gwamna Peter Mbah na Enugu ya koma jam’iyyar APC
Police Arrest 248 Suspects, Recover Weapons and Drugs in Kano Crackdown
Akwa Ibom Police Command Warns Against Jungle Justice, Praise Doctor’s Heroism
Sen. Mohammed Sani Musa Emerges Consensus Candidate for Niger East as Gov. Bago Resolves APC Dispute
Why Senator Musa Emerged as Consensus Candidate
Governor Yusuf Approves 166 Solar-Powered Boreholes to Ease Water Stress in Kano
Barau Emerges APC Candidate for Kano North, Urges Support for Tinubu, Abba