Darakta Janar na Hukumar, Alhaji Lamin Rabi’u Danbappa, ya bayyana cewa wa’adin karɓar kuɗaɗen ya ƙare ne a ranar Juma’a, 5 ga Disamba, 2025.
Ya ce, bayan kammala taro da Hukumar Alhazai ta Ƙasa (NAHCON) an Abuja ranar Alhamis da ta gabata, ba a samu ƙarin wa’adi ba wajen karɓar kuɗin.
Alhaji Lamin Rabi’u Danbappa ya bayyana hakan ne yayin taron da ya gudanar da dukkan masu ruwa da tsaki a Hukumar.
Ya yi bayanin cewa rufe karɓar kuɗin da wuri ya zama dole ne sakamakon sabbin ƙa’idoji da dokoki da hukumomin Saudiyya suka gabatar domin gudanar da aikin Hajjin 2026.
Sabbin ƙa’idojin sun tanadi tsauraran matakai da bukatar kammala shirye-shiryen gudanar da aikin Hajji tun da wuri, domin tabbatar da tafiyar da al’amura yadda ya kamata ga masu niyyar zuwa.

TARON KOYAR DA KIWON KAJI DA KIFI: KPA
Dalung yayi Alhinin halin da Nigeria ke Ciki .
Manoma sun Kira ga Gwamnati Tarayya tayi taka Tsan-Tsan
Gwamna Peter Mbah na Enugu ya koma jam’iyyar APC
Gwamna Buni ya naɗa tsohon ɗan majalisar wakilai, Ismail Gadaka a matsayin sabon sarkin Gudi
Ambassador Dr. Amina Umar Namadi: A First Lady Defined by Compassion, Service, and Humanity
Police Rescue Abducted Three-Day-Old Baby, Arrest Two Suspects in Nasarawa
Governor Yusuf Mourns Alhaji Nuhu Dantani
ADC Leaders Reject INEC Decision, Vow to Resist, Mobilise Support in Otukpo
Police Disburse ₦9.26m to Families of Fallen Officers in Kano