Babban Sakataren kula da iyakokin ruwa na duniya, Mr Kitack Lim ya jinjinawa hukumar NIMASA da na rundunar sojin ruwan kasar nan bisa ga hadin gwiwar su da sauran abokan hulda na kasashen ketare wajen yaki da aikata laifuka akan iyakokin ruwan kasar nan.
Mr Kitack Lim yayi wannan yabon ne a wajen taron karawa juna sani akan iyakokin ruwa wanda ke ci a halin yanzu a birnin Ikko.
KARANTA WANNAN MA:AN YABAWA HUKUMAR NIMASA BISA TAFIYA DA MATA
A sanarwar da mataimakin darakta a sashin hulda da jama’a na hukumar ta NIMASA Mr Edward Osagie ya rabawa manema labarai, yace babban sakataren ya bada tabbacin cewa kungiyar za ta cigaba da goyon bayan Nijeriya a kokarin ta na samar da tsaftacaccen teku da inganta hada-hadar sufurin jiragen ruwa.
Ya kuma bukacin yin hadin gwiwa wajen samar da tashan jiragen ruwa daya tilo ga Afrika maso yamma da kuma Afrika ta tsakiya.
Mr Lim ya kuma kawo shawarar karawa mata guraben ayyuka a bangaren iyakokin ruwan kasar nan, inda yayi nuni da cewa a saboda haka ne ake sa ran yin bikin ranar mata masu aiki a bangaren iyakokin ruwa na duniya a shekara mai kamawa.

Murtala Sule Garo yafi kowa Cancantar Zama Mataimakin Gwamnan Kano.
Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta sanar da rufe karɓar biyan kuɗin Hajji na shekarar 2026.
TARON KOYAR DA KIWON KAJI DA KIFI: KPA
Dalung yayi Alhinin halin da Nigeria ke Ciki .
Manoma sun Kira ga Gwamnati Tarayya tayi taka Tsan-Tsan
Gwamna Peter Mbah na Enugu ya koma jam’iyyar APC
Governor Radda Calls for Collective Action to Tackle Breast Cancer
KNUPDA TASKFORCE COMMITTEE COMMENDED FOR INTENSIFIED ENFORCEMENT EXERCISE ACROSS KANO METROPOLIS.
KANO GOVERNMENT CONSIDERS ESTABLISHING STATE-OWNED AIRLINE TO BOOST REVENUE, SUPPORT DEVELOPMENT
Allegations of bias shake Kano Judicial System as family questions detention of minor
Northern Youth Assembly Applauds National Assembly’s Historic passage of State Police Bill
Governor Uba Sani Appoints Musa Gambo I lallai as Kaduna State Accountant General