Menu

Ma’aikatan Gidan Rediyon Nagarta Sunyi Zanga Zanga kan Rashin Biyansu Albashi

Admin 4 years ago

Ma’aikatan gidan rediyan Nagarta kaduna sunyi zanga zanga bisa rashin biyan su albashi na tsawan wata da watanni da rashin ingantaccen shugabanci da suka yi zargin ana gudanarwa.

Masu zanga zangar dauke da kwalaye sunyi rubutu daban daban inda suke zargin shugaban gidan rediyan da rike musu albashi na watanni biyar.

A cewarsu duk da tarin kudin da gidan rediyan ke samu amma ba’a iya biyan su hakkukin su kamar yadda ya dace.

Sai dai a martanin sa, shugaban gidan radiyan Alhaji Abdulmalik Addiy ya ce basukan da suke bin hukumomi da ma’aikatun gwamnati ya sa suke karancin kuɗaɗe a gidan radiyan.

Amma yanzu abubuwa sun fara daidaita kuma tuni suka fara sauke nauyin da ke kan su na biyan albashin ma’aikata.