Menu

2023: Musa Ilyasu Kwankwaso ya ajiye mukaminsa don neman takara

Admin 4 years ago

By Adnan Abdullahi

Kwamishinan Ma’aikatar Raya karkara ta Jihar Kano Dr Musa Iliyasu Kwankwaso ya ajiye mukamin sa na Kwamishina domin Cika Umarnin Gwamna Ganduje.Da yake Zantawa da Kadaura24 Hon. Musa Iliyasu Kwankwaso yace ya ajiye mukamin nasa ne domin yana da sha’awar yin takarar Dan Majalisar wakilai a Kananan Hukumomin kura madobi da Garun mallam a zabe Mai zuwa.

” Ni dama tun tuni na ajiye mukamina na Kwamishina kamar yadda Sabuwar Dokar Zabe ta bukata, Kawai ban baiyana bane sai yau” inji Musa Iliyasu Kwankwaso

Tsohon Kwamishinan yace Ina fatan Zai Zama Dan takarar Majalisar wakilai da zai wakilci Kananan Hukumomin kura madobi da Garun mallam a jam’iyyar da ta APC .Idan za’a iya tunawa a safiyar lahadin nan ne aka wayi gari da Sanarwar da take Umarni ga Masu rike da mukamai a gwamnatin kano dasu ajiye mukamansu Matukar suna da sha’awar tsayawa takara a baze Mai Zuwa