Menu

Ramadan: Adamu Abubakar Gwarzo Foundation Ta Tallafawa mabukata sama da 5000 da kayan Abinci

Admin 4 years ago

Daga Abdullahi Sufi


Cikin Goma (10) farkon Ramadan Adamu Abubakar Gwarzo Foundation -AAG-Foundation karkashin tsarin gudanarwar Professor Adamu Abubakar Gwarzo yayi nasarar rabon Abinci da sauran Alherai ga iyalai sama da 5000 a Kasar Nigeria 🇳🇬  da Jamhuriyar Niger 🇳🇪 
Rabon an yi shine wajen tsarin zakulo mabukatan cikin mabukata ko takakan Talaka Gida da bisa titi wajen basu abin kyautar. 
Wasu cikin garuruwa da akai wannan lamari sun hada da;
Nigeria 🇳🇬 1- Sokoto2- Adamawa3- Katsina 4- Kano5- Jigawa
Niger 🇳🇪 1- Maradi2- Dan Issa 
Rabon anyi ba hoto Bisa umarnin President MAAUN Sai dai wasu daga Masu bukatar sun dauka. 
Muna sa ran wasu cikin su zasu Bawa wasu tallafi suma, shekara Mai zuwa In Sha Allah.
Rohotanni sun tabbatar da samun bibiyar neman Karin bayani da sha’awar bada gudummawa ga mabukata bayan gudanar da shiri na musamman a Radiyo Garkuwa, Maradi, Niger. 
Allah ya jikan Mahaifin Prof Gwarzo ya karawa Mama lafiya, ya gafarta wa iyayen mu baki daya Amin.
Wannan itace addu’ar da wadanda suka amfana da dangin su suna sukai tayi.
An nemo mabukatan cikin mabukata don taimaka musu a yayin taimako hakan zai kara tabbatar da samar da tallafi ga wadanda ya dace a bawa.