Hukumar kula da iyakokin ruwan kasar ta kaddamar da manhajar zamani ga ma’aikatan iyakokin ruwan kasar don saukaka da kuma inganta ayyukan su.
Mataimakin darakta a sashin hulda da jama’a na hukumar, Mr Edward Osagie ne ya bayyana haka a sanarwar da ya rabawa manema labarai a birnin ikko.
Sanarwar ta ce Shugaban hukumar, Dr Bashir Yusuf Jamoh ya bayyana kaddamar da manhajar a matsayin wata hanyar zamanatar da ayyukan ma’aikatan iyakokin ruwan kasar nan, inda yayi nuni da cewa hakan zai taimaka matuqa kuma ya kasance wani kundi na adana bayanan ma’aikatan iyakokin ruwan kasar nan.
Shugaban hukumar wanda Engineer Victor Ochei ya wakilta yace manhajar zata kuma taimakawa ma’aikatan wajen yin tsimi da kuma inganta ayyukan su.
Ana kuma sa ran manhajar ta zamani zata saukaka samar da shaidar katin aiki na zamani ga ma’aikatan.
Dr Bashir Yusuf Jamoh ya kuma jaddada aniyar hukumar wajen tabbatar da cewa ma’aikatan hukumar suna samun horo akai-akai don bangaren iyakokin ruwan kasar nan tayi gogayya da sauran takwarorin ta na duniya.
A nashi tsokacin, Shugaban kungiyar ma’aikatan iyakokin ruwan kasar nan, Comrade Adewale Adeyanju bayyana farin cikin shi yayi dangane da samar da wannan manhaja ta zamani, sannan ya yabawa hukumar NIMASA bisa kokarin ta wajen inganta ayyukan bangaren iyakokin ruwan kasar nan da ma’aikatanta ta hanyar basu horo yanda ya kamata.
Taron ya samu halartar wakilan manyan masu ruwa da tsaki a bangaren harkar iyakokin ruwa, da na masu dakon jiragen ruwa, da na masu fito na kasa, da na masu kula da shige da fice na kasa, da na hukumar hana fasa kwauri na kasa, sai kuma wakilin kwamishinan ‘yan sanda na tashar ruwan Apapa da sauran manyan baki.

Murtala Sule Garo yafi kowa Cancantar Zama Mataimakin Gwamnan Kano.
Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta sanar da rufe karɓar biyan kuɗin Hajji na shekarar 2026.
TARON KOYAR DA KIWON KAJI DA KIFI: KPA
Dalung yayi Alhinin halin da Nigeria ke Ciki .
Manoma sun Kira ga Gwamnati Tarayya tayi taka Tsan-Tsan
Gwamna Peter Mbah na Enugu ya koma jam’iyyar APC
Sharada Joins Kano Central Senatorial Race, Calls for Free and Fair APC Primaries
NEPC trains SMEs, MSMEs in Kano to boost export readiness
Traditional institutions key to security, peace building in Nigeria, security – CAS
Air Chief tasks commanders to decisive airstrikes against bandits, terrorists
Tinubu Meets Senator Sani Musa, Commends Support for Reform Agenda
Datti Baba-Ahmed Defects to PRP, Picks Membership Card in Zaria