Daga Abdullahi Alhassan Kaduna,
Ganin yarda zaben shekara ta 2023 ke kara karatowa, shugaban kungiyar Atiku Gida-gida,wato Atiku door to door mobilization forum,a turance Ambassada Imran Abdullahi.
Yace ƙungiyar su ta lashi takobin samarwa Atiku Abubakar kuri’a har miliyan goma sha biyar a fadin kasar nan,da aka tambaye shi ko yaya zai yi ganin cewa a kwai sauran jamiyu sai yace “munada mambobi da suka kai Kimanin dubu a shirin a fadin kasar nan.
Wanda a halin yanzu mambobin mu sun dukufa wajen wayar wa jama’a kai da muke zuwa gida -gida da zummar wayar musu da kai kan kudorori da manufofin shugaban ƙasa mai zuwa in Sha Allahu wato Atiku Abubakar, fidda Najeriya na halin da take ciki, wanda ya kudurci zai hada kan yan Najeriya.
Shugaban kungiyar yana wan nan jawabin ne a taron kaddamar da mambobin kungiyar reshen jihar Kaduna.
Inda ya kara da cewar su suna goyon bayan shi ne saboda kudirin shi ne na bawa Matasa kaso 40 na mukamai ga matasa ldan Allah ya ida nufi.
Shi kuwa a nashi jawabin shugaban kungiyar Atiku village to village, to kauye zuwa kauye,Abdulbasid Gaini cewa yayi sun dukufa wajen wayar yan Najeriya kai, musamman ma mutanen kauyuka kan kudirin Atiku na samar da tsaro a yankunan karkara, ka san cewar mutanen karkara su noma da kiwo suka sani wanda a halin yanzu babu tsaro a yan kunan su.
Ya kuma kara da cewa manufofi na Atiku Abubakar kan matasa ne yana muke goyon bayan shi na zama shugaban ƙasa,”ka dai ga mu matasa ne,amma muna mara masa baya ,na ganin ya zama shugaban kasar nan,In Allah ya yarda.
Shugaban kungiyar ya kara cewar muna fatan Atiku zai samar da tsaro a yankunan karkara da zai bama yan’uwan mu damar aikin su na noma da kiwo ba tare da fargaba ba ,kamar yarda ake ciki yanzu haka musamman ma yan kunan kasar nan.

Murtala Sule Garo yafi kowa Cancantar Zama Mataimakin Gwamnan Kano.
Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta sanar da rufe karɓar biyan kuɗin Hajji na shekarar 2026.
TARON KOYAR DA KIWON KAJI DA KIFI: KPA
Dalung yayi Alhinin halin da Nigeria ke Ciki .
Manoma sun Kira ga Gwamnati Tarayya tayi taka Tsan-Tsan
Gwamna Peter Mbah na Enugu ya koma jam’iyyar APC
CP Azare Commends Peaceful Conduct of APC Primaries in Akwa Ibom
Kano South Fallout: Has Rurum Drawn a Red Line Against Kawu Sumaila?
When Ja’o’ji Answers Reconciliation With Humility in Victory
APC Aspirant Raises Concerns Over Conduct of Primary Election in Jigawa Constituency
Kano Govt Pledges Stronger Collaboration with FG, Partners on Education
Ambassador Dr Amina Umar Namadi Sponsors Mass Marriage for 300 Couples in Jigawa