Menu

2023 : Zamu Dora a Akan Ayyukan Cigaban Alumma Da Ganduje ya yi – Garo

Admin 4 years ago

Daga Abdullahi Kano

Dan Takarar mataimakin Gwamna Karkashin Tutar Jam’iyyar APC a kakar Zabe Mai Zuwa Alhaji Murtala Sule Garo ya ce Idan Allah ya Lamunce Aka Zabe su,a zaben gwamnan da ke tafe to za su dora ne akan ayyukan raya kasan da gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya faro.

Alhaji Murtala Sule Garo ya Bayyana haka ne lokacin da yake zantawa da manema labarai a kano.

Yace Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya yi matukar kokari ta fannin sauya rayuwar alummar jihar kano, kuma in har alummar kano suka bamu dama ta hanyar zaben mu to babu shakka ba zamu basu kunya ba.

Murtala Garo ya kara da cewar bunkasa cigaban ilmi, lafiya, noma ta tallafawa matasa don su zamo masu dogaro da kawunansu na data cikin bangarorin da zamu fi baiwa fifiko.

“Babban abin da zamu sa a gaba in Allah ya bamu nasara shi ne inganta rayuwar alummar mu”

Sanin kowa ne gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya bullo da shirin nan na ba da ilmi kyauta kuma dole, babu shakka geamnatinmu za ta dora akan hakan in Allah ya bamu nasara.

Munyi tsarin samar da ingatattun dakunan shan magani a dukkan mazabu 484 da ke fad in jihar kano.

Dan takarar mataimakin gwamnan yace sun kuma yi shirin kawo sabbin na’urorin noma na zamani don tallafawa manoma, wanda hakan zai kara bunkasa samar da abinci da karin guraben ayyukanyi a jihar kano.

Garo ya kuma ba da tabbacin cigaba da yin tituna a yankunan karkara da birni don saukakawa manoma fito da amfanin  gona zuwa kasuwanni, wanda hakan zai kara Habaka tattalin arzikin jihar.

” ba zamu yi kasa a gwiwa ba wajen baiwa matasa jari tare da koyar da su sanaoin dogaro da Kai, don su dogara da kansu,    harma su dauki wasu aiki”