Menu

HUKUMAR KULA DA IYAKOKIN RUWAN KASAR NAN TAYI ALLAH WADAI DA ZANGA-ZANGAR DALIBAI A KASAR PHILIPPINES

Admin 4 years ago

Hukumar kula da iyakokin ruwan kasar nan wato NIMASA tace tana nazarin faifan bidiyon dake yawo a shafukan sada zumunta na zamani dake nuna yanda wasu dalibai sukayi zanga-zanga a ofishin jakadancin Nijeriya dake kasar Philippines.

A wata sanarwar da ta samu sa hannun mataimakin darakta a sashin hulda da jama’a na NIMASA, Mr Edward Osagie, kuma aka rabawa manema labarai, yace hukumar ta samu sahalewar ma’aikatar sufuri don ziyarar gani da ido zuwa Philippines da zimmar gano musabbabin zanga-zangar, don gano bakin zaren.

Sanarwar tayi bayanin cewa Babban Darakta mai kula da hada-hadar sufurin jiragen ruwa a hukumar, Injiniya Victor Ochei ne ake sa ran zai jagoranci ziyarar zuwa kasar ta Philippines don gano hanyar warware matsalar cikin ruwan sanyi.

Sanarwar tayi Allah wadai da wannan abin kunya da wadancan dalibai su kayi, sannan hukumar ta bukaci jama’a da su guji yada jita-jita har sai an gano musabbabin zanga-zangar.

Ana sa ran gabatar da rahoto a hukumance daga NIMASA da zarar an kammala ziyarar aikin gani da idon.