Menu

KUNGIYAR KWARARRU MASU HADA-HADAR SUFURI TA KASA TA DAKATAR DA BABBAN ZABEN TA

Admin 4 years ago

Shugabannin kungiyar kwararru masu hada-hadar sufuri ta kasa ta sanar da dakatar da zaben da tayi shirin gudanarwa.

Shugaban kwamitin zabe na kungiyar, Farfesa Innocent Ogwude ne ya shaidawa manema labarai hakan a Abuja.

A cewar shi, Shugaban kungiyar Dr Bashir Jamoh da kuma sakataren kungiyar ta kasa Mr Chinda Evans Ogbuji sun sanya hannu a taron gaggawa na majalisar zartaswan kungiyar, inda suka bayyana cewa dakatar zaben yayi daidai da tsarin dokokin kungiyar.

Yace majalisar zartaswan ta dakatar da zaben ne don sake tsare-tsaren gudanar da sahihin zaben da zai samar da sabbin shugabannin kungiyar.

Dr Bashir Yusuf Jamoh yayi kira da kwamitin zaben da su guji son rai, kuma kada su yarda wani ya tilastasu wurin yin ba daidai ba, wanda a cewar shi, yin haka zai zubar da kimar kungiyar a idon jama’a.

Ya kuma jaddada aniyar kungiyar na baiwa ko wane dan takara dama, ba tare da tsangwama ba, inda yayi nuni da cewa kungiyar ba za ta lamunci karya dokokin da ke kunshe a tsarin dokar kungiyar ba.

Ita dai wannan kwamitin zabe dake karkashin Farfesa Innocent Ogwude na da alhakin gudanar da zabe ne a taron shekara-shekara na kungiyar da aka sa ran yi a karshen makon watan Nuwamba mai zuwa.