Menu

“Jamilu Isyaku Gwamna Ne Ya Fi Dacewa Da Zama Gwamnan Jihar Gombe 2027 Duba Da Ƙwarewarsa Kan Aikin Gwamnati Da Harkokin Tattalin Arziƙi”, In Ji Shawai

Admin 22 hours ago 0

‎A cewar mai magana da yawun ɗan takarar gwamnan, Ibrahim Sani Shawai, Dr. Jamilu Gwamna gogagge ne ta fuskar aikin gwamnati da sanin harkokin tattalin arziƙi da zuba jari.

‎Shawai ya ce tattaunawa kan siyasar Gombe gabanin zaɓen 2027 bai kamata ta tsaya kan neman mulki da kalaman siyasa ba kawai, sai an duba ƙwarewar ƴan takara wajen tafiyar da tattalin arziƙin jihar, kamar yadda Dokin Ƙarfe TV ta ruwaito.

‎”Gombe na buƙatar shugaba mai fahimtar zuba jari, kasuwanci, haɗin gwiwar gwamnati da kamfanoni masu zaman kansu, samar da ayyukan yi da bunƙasa harkokin noma da fasahar zamani”. In ji shi.

‎Ya kuma bayyana cewa Jamil Gwamna ya taɓa zama Shugaban Hukumar Ruwa ta Jihar Gombe tare da samun gogewa a masana’antar rarraba wutar lantarki ta Najeriya.

‎Shawai ya ce irin wannan ƙwarewa za ta taimaka wajen sauya tattalin arziƙin Gombe daga dogaro da gwamnati zuwa tattalin arziƙi da noma, kasuwanci, fasaha, zuba jari wanda kamfanoni masu zaman kansu za su taka muhimmiyar rawa.

‎”Tambayar da ya kamata a yi a 2027 ba wai waye yake son zama gwamna ? ba ce, sai dai waye yake da ƙwarewar gudanar da gwamnati da tattalin arziƙin Gombe ?”, In ji shi.

‎Shawai ya kuma ƙara da cewa Dr. Jamil Gwamna na wakiltar shugabanci da ya ginu kan ƙwarewa, cancanta da hidimar jama’a.

Leave a Reply

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *