Jami’ar harkokin sufurin jiragen ruwa ta duniya ta yabawa hukumar NIMASA bisa tafiya da mata da kuma basu damar baje fasahar su ta hanyar tura su kasashen ketare don karo ilimi.
A wata sanarwar da mataimakin darakta a sashin hulda da jama’a a hukumar, Mr Edward Osagie ya rabawa manema labarai a birnin Ikko yace yabon ya fito ne daga bakin Shugabar Jami’ar, Dr Cleopatra Doumbia-Henry a lokacin da ta kawo ziyara a shedikwatar hukumar don tattaunawa akan batun inganta horas da ma’aikatan NIMASA.
Dr Cleopatra Doumbia-Henry tayi bayanin cewa maqasudin ziyarar ita ce don karfafa hadin gwiwa tsakanin jami’ar da NIMASA da kuma lalubo sabbin hanyoyin kyautata dangantaka.
Shugabar Jami’ar har ila yau ta kuma yaba da karin mata da aka tura su jami’ar don zurfafa ilimin akan harkokin sufurin jiragen ruwa.
A nashi bangaren, Shugaban hukumar kula da iyakokin ruwan kasar nan, Dr Bashir Yusuf Jamoh yace dadaddiyar alaqar dake tsakanin hukumar da jami’ar ta samo asali ne bisa ga burin da hukumar take da shi wajen inganta kwarewa ta fuskar bincike don don ciyar da hukumar gaba.
Ya kara da cewa hukumar na da burin cigaba da karfafa gwiwar mata shiga a dama da su a bangaren harkokin iyakokin ruwa da kuma sufurin jiragen ruwa.
Dr Bashir Jamoh ya jaddada aniyar hukumar wajen cigaba da horas da ma’aikatanta don inganta kwarewar jami’an ta a bangaren iyakokin ruwan Nijeriya.

Murtala Sule Garo yafi kowa Cancantar Zama Mataimakin Gwamnan Kano.
Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta sanar da rufe karɓar biyan kuɗin Hajji na shekarar 2026.
TARON KOYAR DA KIWON KAJI DA KIFI: KPA
Dalung yayi Alhinin halin da Nigeria ke Ciki .
Manoma sun Kira ga Gwamnati Tarayya tayi taka Tsan-Tsan
Gwamna Peter Mbah na Enugu ya koma jam’iyyar APC
Traditional institutions key to security, peace building in Nigeria, security – CAS
Air Chief tasks commanders to decisive airstrikes against bandits, terrorists
Tinubu Meets Senator Sani Musa, Commends Support for Reform Agenda
Datti Baba-Ahmed Defects to PRP, Picks Membership Card in Zaria
AI crucial for accountability in Nigerian varsities, says EFCC Chairman
National Development: Emir Sanusi urges universities to drive AI policy