A Wani Abu da ba’a saba ganin masu rike da madafun iko (Zababbu ko Nadaddu) nayi ba, Dan majalisar wakilai mai wakiltar kananan hukumomin Rano, Kibiya da Bunkure *RT Hon Kabiru Alhassan Rurum* ya fitar da kudi Miliyan 22 da dubu dari 5 da aka fara rabawa rukuni daban daban na Al’ummar kananan hukumomin sa a matsayin Barka da Sallah don suji dadin yin bukukuwan Sallah Babba..
Dan Majalisar ya Kuma fitar da Buhunan Shinkafa dubu 1 da za’a hadawa Mutane a wannan rabon saboda a girka abinci Sallah aci a baiwa makota..
Cikin wata sanarwa da mataimaki na musamman ga Rurum din kan harkokin Yada Labarai Fatihu Yusuf Bichi ya fitar a litinan din nan yace ‘Dan majalisar yayi hakan ne da nufin Sanya farin cikin da Annashuwa a zukatan Al’ummar Mazabarsa tasa a wannan lokaci da ake Shirin yin Bikin sallah ga Kuma kakani kayin rayuwa da ake ciki.
Kowacce Karamar hukuma mutane 550 ne zasu amfana da kudaden da za’a raba Wanda a kananan hukumomin guda 3 ya kama zunzurutun kudi naira Miliyan 16 da dubu dari 5..
Akwai Kuma rukunin Matasa da ‘Yan Social Media da Mata da za’a rabawa wata naira Miliyan 2 sannan Kuma akwai Raguna guda 50 da aka siyo za’a rabawa Limanan Masallatan Juma’a na kananan hukumomin dan suyi layya.
Tuni Al’ummar Karamar hukumar Bunkure da aka fara rabon dasu a yau suka bayyana godiya da Jin dadinsu ga Dan Majalisar nasu da sukace baya gajiya wajen hidimta su…
Ko a lokacin Azumi kusan tan 6 na Shinkafa RT Hon Kabiru Alhassan Rurum ya rabawa Al’ummar kananan hukumomin nasa sannan a karshe ya bada Atamfofi da Shaddoji da kudin dinki ga fiye da mutane dubu 2 suyi shagalin Sallah…
*Fatihu Yusuf Bichi*
*Senior Special Assistant on Media & Publicity to Rt Hon Rurum*
*Member Representing Rano, Kibiya & Bunkure Federal Constituency, HOR Abuja.*
*June 2nd, 2025.*d

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta sanar da rufe karɓar biyan kuɗin Hajji na shekarar 2026.
TARON KOYAR DA KIWON KAJI DA KIFI: KPA
Dalung yayi Alhinin halin da Nigeria ke Ciki .
Manoma sun Kira ga Gwamnati Tarayya tayi taka Tsan-Tsan
Gwamna Peter Mbah na Enugu ya koma jam’iyyar APC
Ambassador Dr. Amina Umar Namadi: A First Lady Defined by Compassion, Service, and Humanity
Police Rescue Abducted Three-Day-Old Baby, Arrest Two Suspects in Nasarawa
Governor Yusuf Mourns Alhaji Nuhu Dantani
ADC Leaders Reject INEC Decision, Vow to Resist, Mobilise Support in Otukpo
Police Disburse ₦9.26m to Families of Fallen Officers in Kano