Menu

ATIKU YA SAKE BADA TABBACIN BAYAR DA KASO 40 NA MUKAMAI GA MATASA DA MATA

Admin 4 years ago

.. YA BAWA MATASA TABBACIN BARIN TARIHI MAI KYAU DA GWAMNATI MAI TAFIYA DA KOWA.

Dan Takarar shugabancin Najeriya na Jam’iyyar PDP a zaben 2023 kuma tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar ya bawa matasan Najeriya tabbacin barin kyakkyawan tarihi gare su, idan aka bashi damar jagorantar al’amuran kasar.

Atiku Abubakar ya bada wannan tabbaci ne yau Laraba 3 ga watan Agusta, Lokacin da ya karbi bakuncin tawagar shugannin PDP sabon karni karkashin jagorancin babban daraktan ta Audu Mahmud a gidan sa dake Abuja.

Dan Takarar shugabancin kasar ya sake jaddada aniyar sa kamar yadda ta ke kunshe cikin kundin manufofin sa, na bawa matasa dama a gwamnatin sa ta hanyar ware musu kaso 40, inda kuma yace zai yi sauye-sauyen da suka Kamata domin bada dama ga mata da matasa.

Wazirin Adamawa ya kara da cewa a gwamnatin PDP ne kawai aka aiwatar da tsarin nan na kebewa mata kaso 35, inda yace APC ba ta taba girmama wannan yarjejeniya ba.

Ya kuma koka game da halin da matasa suka sami kansu, inda ya yi alkawarin daidaita al’amuran. A saboda haka, yace ilimi zai zamo babban ginshikin gwamnatin sa domin bunkasa rayuwar matasa da habaka dimukuradiyya. Ya bayyana takaici kan yadda APC ta wargaza tsarin da gwamnatin PDP ta shimfida a baya.

Yayin da yake tabbatar da muhimmancin matasa Wajen Gina kasa, Dan Takarar na PDP ya jaddada cewar zai yi aiki da bukatun zamani, tare da gudanar da gwamnati Mai tafiya tare da kowa Mai la’akari da banbance-banbancen dake tsakanin mu.

A nasa jawabin, jagoran ayarin, Audu Mahmud yace Atiku Abubakar wata mabubbuga ce ta karfafa gwiwa da kyakkyawan tunani ga matasan kasar nan, inda ya bayyana yakinin da yake da shi na kwarewar Atiku domin magance matsalolin tattalin arziki da matsalolin siyasa domin amfanin dukkan yan Najeriya.

Abdulrasheed Shehu
Mataimaki na Musamman ga Mai girma Atiku Abubakar kan kafafen yada labarai.

3 ga Agustan 2022.