Daga Abdullahi Alhassan, Kaduna
A yunkurin su na ganin an samar da wada taccen abinci ga yan Najeriya, musamman ma abubuwan yau da kullum,da kullum ake sarrafawa don abinci, Manajan Kasuwanci na Kamfanin fulawa wato Golden Penny, a Kaduna Mista lsrael Obafemi yace kanfanin su ya samar da ton 30 na Masara, Alkama,da Dawa don amfanin magidanta a shiryar arewa masu yamma da ma arewa masu gabas wanda muke kira Masalina,Dawavita, MasaFlour da ma Masavita.
Mista Obafemi yana wannan jawabi ne a Kaduna yayin kaddamar da sabon samfurin garin masara da alkama irin sa na farko a Najeriya don masu yin waina da sauransu ya kara da cewar irin wannan samfurin zai kawo tsadar Biredi a ƙasar nan ganin cewa jama’a da dama sun karkata ne kan biredi ne don kalaci maimakon sarrafa garin masara ko alkama.
Manajan Kasuwancin shiryar ya kara da cewar shi wan nan sabon samfurin na hade ne da garin masara da fulawa ,da kuma keda sauƙin sarrafawa ga masu amfani dashi akan bukatu daban-daban.
Mista Israel ya ce wan nan kyakkyawan tsari ne da zai magance matsalolin haukawar farashi kayan abinci kamar masarar dawa dama alkama,Kasan cewar su abubuwan amfani na kullum ne, kaga da wan nan sabon samfurin zai kawar da ƙaruwar tsadar Biredi da saurasu saboda samun mafita ne gasu masu amfani da kayayyakin.
Shi kuwa wani dan kasuwa dake Kaduna Alhaji Abdulsalam Abdulrazak, cewa ya yi kimanin shekaru 30 kenan yana hudda da kamfanin kuma zasu cigaba da harka da kamfanin kasancewar sa suna samar da kayeyyaki cikin farashi mai rahusa tare kuma da kyautata kayeyyaki cikin da ya yi dai-dai da al’ummar mu.

Amincin Tinubu Ga Barau Kan Harkar Tsaro Da Cigaban Kasa
Shugaban Ƙaramar Hukumar Kabo Hon. Lawan Najume Kabo ya sauke Sakataren Mulki na Karamar Hukumar da nadaddun Kansiloli huɗu, Saboda Shiga Ƙungiyar Tallata Shugaba Tinubu Da Sanata Barau (TMS) a Jihar Kano .
Murtala Sule Garo yafi kowa Cancantar Zama Mataimakin Gwamnan Kano.
Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta sanar da rufe karɓar biyan kuɗin Hajji na shekarar 2026.
TARON KOYAR DA KIWON KAJI DA KIFI: KPA
Dalung yayi Alhinin halin da Nigeria ke Ciki .
Bauchi governor warns new LG chairmen against mismanagement of fund.
Dangote Marks Youth Day, Strengthens Skills, Social Footprint At Obajana
Infrastructural Development, Free And Fair Osun Elections, Enough Reasons For Tinubu 2nd Term, Kwankwaso
NDLEA Arrests 80 Suspects, Dislodges 16 Drug Joints in Kano
Kano Govt Faults TRACKA Report on ₦235.4m School Project
Kano Committee Arrests Ex-Council Chairman Over Alleged Fentanyl Sales