Rundunar ƴan sandan Najeriya reshen Jihar Yobe ta kama mutum uku da zargi da fashi da makami da fasa gida domin sata.
A wata sanarwa da mai magana da yawun yan sanda reshen Jihar Yobe ASP Dungus Abdulkarim ya fitar, cikin wadanda ake zargi har da wani soja da ke ƙarƙashin rundunar Operation Hadin Kai.
Tunda farko mutanen uku dai sun fasa gidan wata mata a Sabon-Pegi da tsakar dare dauke da muggan makamai ciki har da bindiga ƙirar AK-47 inda suka sace kudi kimanin naira 250,000 haka kuma suka sace mota ƙirar Peugeot 307 da wayar salula Nokia.
Sai dai bayan ƴan sanda sun samu labarin wannan lamari, sai suka shiga aikin nemansu har suka kama su.
Tuni waɗanda ake zargin suka amsa laifukan da ake zarginsu da aikatawa

Murtala Sule Garo yafi kowa Cancantar Zama Mataimakin Gwamnan Kano.
Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta sanar da rufe karɓar biyan kuɗin Hajji na shekarar 2026.
TARON KOYAR DA KIWON KAJI DA KIFI: KPA
Dalung yayi Alhinin halin da Nigeria ke Ciki .
Manoma sun Kira ga Gwamnati Tarayya tayi taka Tsan-Tsan
Gwamna Peter Mbah na Enugu ya koma jam’iyyar APC
Dignitaries Gather in Abuja to Honour Late Buhari One Year After His Death
FG Suspends Proposed ₦50,000 WAEC, NECO Registration Fee Increase
Gov. Yusuf Nominates Deputy Garo as Running Mate for 2027 Governorship Election
Police to Arraign Man Over Alleged Fake Presidency Agency
Atiku Criticises Planned Increase of WAEC, NECO Examination Fees to N50,000