Menu

Takarar Gwamna ta ba na a mutu ko ayi rai ba ne – Shugaban NIMASA

Admin 4 years ago

Darakta-Janar na hukumar kula da harkokin sufurin jiragen ruwa ta Najeriya, Dr Bashir Yusuf Jamoh, ya ce har yanzu bai fito fili ya bayyana aniyarsa ta takarar gwamnan jihar Kaduna a hukumance ba.

Sai dai shugaban ya bayyana cewa bai kawar da yiwuwar yin aiki da kiraye-kirayen mutanensa ba idan sun ga ya dace ya tsaya takarar.

Da yake amsa tambayoyin manema labarai a Zariya, Dr Jamoh ya ce ko da ya gamsu ya tsaya takarar ‘ba na a mutu ko a yi rai ba ne’.

Shugaban ya ce, “Ba zan nace cewa dole ne in zama gwamna ‘ko ana ha maza ha mata ba’. Amma zan so in yi wa jama’ata hidima kuma in kai ga iyakar abin da suke tsammani.”

Ya kara da cewa mutane da kungiyoyi da dama daga kananan hukumomi 23 na jihar suna ci gaba da tuntubar sa domin ya tsaya takara.

Dr Jamoh ya ce nan ba da jimawa ba za a bayyana matsayinsa idan ya kammala shawarwarin nasa.

Shugaban NIMASA ya ci gaba da cewa abin da gidauniyarsa ke yi ya bambanta da duk wani buri na siyasa, kamar yadda aka yi a cikin shekaru biyu da suka gabata.

“Jamoh Foundation na da burin inganta zamantakewar jama’a musamman ma wadanda aka zalunta a matsayin hanya ta na tallafaw jama’a kamar yadda suka Dade suna yi min kara.

“Gidauniya tana bayar da tallafin ilimi ga matasa, gudanar da aikin jinya da bayar da tallafin noma ga ‘yan kasa,” in ji shi.

1 Comment

1 Comment

  1. Zainab lawal says:

    Masha Allah, muna bayanka, hundred percent Inshaallahu

Comments are closed.