Dan majalisar wakilai mai wakiltar karamar birni da kewaye a jihar kano, Shaaban Ibrahim Sharada, ya sauya sheka daga jam’iyyar APC zuwa jam’iyyar ADP.
Bayan sauya sheka, DAILY NIGERIAN ta rawaito cewa dan majalisar ya koma jam’iyyar ADP kuma ya karbi tikitin takarar gwamna na jam’iyyar.
Majiya mai tushe daga hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa, ofishin INEC dake Kano, ta ce Shaaban sharada zai yiwa jam’iyyar ADP takara tare da abokin takararsa, Rabiu Bako.
Hon. Shaaban Sharada wanda shi ne shugaban kwamitin majalisar wakilai kan harkokin tsaro da leken asiri, ya yi takarar neman tikitin takarar gwamna a jam’iyyar APC amma mataimakin gwamnan jihar Nasiru Gawuna ya kayar da shi.
Kadaura24 ta rawaito Dan majalisar ya kasance cikin kungiyar G-7, a jam’iyyar APC karkashin jagorancin tsohon Gwamna Ibrahim Shekarau.
Asalin Labari… kadaura24

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta sanar da rufe karɓar biyan kuɗin Hajji na shekarar 2026.
TARON KOYAR DA KIWON KAJI DA KIFI: KPA
Dalung yayi Alhinin halin da Nigeria ke Ciki .
Manoma sun Kira ga Gwamnati Tarayya tayi taka Tsan-Tsan
Gwamna Peter Mbah na Enugu ya koma jam’iyyar APC
Ambassador Dr. Amina Umar Namadi: A First Lady Defined by Compassion, Service, and Humanity
Police Rescue Abducted Three-Day-Old Baby, Arrest Two Suspects in Nasarawa
Governor Yusuf Mourns Alhaji Nuhu Dantani
ADC Leaders Reject INEC Decision, Vow to Resist, Mobilise Support in Otukpo
Police Disburse ₦9.26m to Families of Fallen Officers in Kano