Menu

Jam’iyyar NNPP ce za ta lashe a Kano – Hon Nafiu Dorayi (Youth Leader)

Admin 3 years ago

Daga Abdullahi Kano

Wani zakakurin dan jam’iyyar NNPP da ke karamar hukumar gwale a kano Honourable Nafi’u Dorayi wanda aka fi sani da youth leader yace jam’iyyar NNPP ce zata lashe zabe daga sama har Kasa a jihar Kano.

Honourable Nafi’u Dorayi ya bayyana hakan ne lokacin da yake fashin baki kan zaben da ke tunkarowa.

Yace jam’iyyar NNPP ta riga at kammala tsare tsare ingatattu wanda zasu yi amfani da su wajen kara bunkasa jin dadi da walwalar alummar jihar Kano.

” zamu bijiro da ingattattun tsari na inganta cigaban ilmi , lafiya, aikin noma, tallafawa matasa da sana’oin dogaro da Kai don cigaban Jihar baki daya.

“Alummar Kano sun gaji da mulkin kama karya, don haka ina da yakinin cewar a wannan karo alummar jihar nan ba zasu sake yadda ayi musu sakiyar da ba ruwa ba”

Honourable Nafiu Dorayi yace muddin alumma kano suka zabi jam’iyyar NNPP fata sama har kasa to lallai ba za su yi da na sani ba.

Bisa haka ne Hon Nafi’u Dorayi ya bukaci masu kada kuria da suyi fitar farin dango ranar zabe son kada wa jam’iyyar NNPP kuri’unsu don fitar da su daga kangin talaucin da suke ciki.