Menu

NAYI JIMAMIN MUTUWAR PELE- Buhari

Admin 3 years ago 0

Daga Nura Zazzau

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya bi sahun shugabannin ƙasashen duniya wajen miƙa saƙon ta’aziyyarsa kan rasuwar fitaccen ɗan ƙwallon duniya Edson Arantes do Nascimento wanda aka fi sani da Pele.

Wannan na kunshene a cikin wata sanarwa da mataimaki na musamman ga shugaban ƙasar kan kafofin yaɗa labarai Malam Garba shehu ya fitar, shugaba Buhari ya bayyana ɗan wasan da cewa mutum ne ”mai kirki da ƙanƙan da-kai, duk da cewa shi babban ɗan wasa ne”.

KARANTA WANNAN:<em>SHUGABA BUHARI YA AMINCE DA BAIWA YAN NIJERIYA RANCEN KUDADE DON MALLAKAR JIRAGEN RUWA</em>

”Pele ya gina kyakkyawar alaƙa tsakanin ƙasashe, da ƙabilu da ma addinai, haƙiƙa duniya ba za ta manta da shi ba”, kamar yadda sanarwar ta bayyana.

Tsohon gwarzon ɗan wasan duniyar ya mutu ne ranar alhamsi bayan ya sha fama da rashin lafiya.

Ya lashe kofin duniya uku tare da zura ƙwallaye sama da 1,281, ya zama zaƙaƙurin ɗan wasan duniya.

Leave a Reply

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *