Wasu da ake zargin ’yan bindiga ne sun kai farmaki a unguwar Gbagy Villa da ke Karamar Hukumar Chikun a Jihar Kaduna, suka kashe mutum daya sannan suka sace wasu 10.
Ya zuwa yanzu dai babu wani cikakken bayani a kan harin da ’yan bindigar suka kai a cikin daren ranar Litini8
Shugaba Buhari ya ceto kasar nan daga durkushewa -Malami
Wani mazaunin unguwar da ya bukaci a sakaya sunansa saboda tsaro ya ce, “Sun shiga gida-gida suka dauki mutane sannan suka kashe wani mutum daya.”
Aminiya ta gano cewa daga cikin wadanda maharan suka sace a yayin harin, akwai mata da kananan yara.
Wani jami’in rundunar tsaron sa-kai (JTF) a yankin ya tabbatar da mutuwar mutum daya a sakamakon harin.
Kwao yanzu dai babu wata sanarwa game da harin daga Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kaduna, kakakinta kuma, ASP Jalige Mohammed, bai samu daukar kiran wayar wakilinmu ba, ballantana mu ji ta bakinsa.
A makonnin da suka gabata ne mazauna unguwannin Juni, Unguwar Gimbiya, Kauyen Oil, Sabon Tasha GRA da Unguwar Barde, duk a Karamar Hukumar Chikun suka fuskanci munanan hare-hare daga ’yan bindiga.
Aminiya

Murtala Sule Garo yafi kowa Cancantar Zama Mataimakin Gwamnan Kano.
Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta sanar da rufe karɓar biyan kuɗin Hajji na shekarar 2026.
TARON KOYAR DA KIWON KAJI DA KIFI: KPA
Dalung yayi Alhinin halin da Nigeria ke Ciki .
Manoma sun Kira ga Gwamnati Tarayya tayi taka Tsan-Tsan
Gwamna Peter Mbah na Enugu ya koma jam’iyyar APC
INEC, Police Strengthen Collaboration for Credible Elections in Akwa Ibom
Police Arrest Suspected Armed Robber, Recover Weapons in Akwa Ibom
NSCDC Arrests Suspected Railway Vandal, Two Impersonators in Kano
Sokoto Executive Council Approves Road, Airport and Transport Projects Worth Billions
Senator Sani Musa Receives Massive Welcome in Suleja, Calls for Unity and Grassroots Development
Imposition of consensus candidate will Tear Taraba APC- Kente warns