Uwar Gidan Shugaban Kasa Aisha Buhari ta ja hankalin gwamnatin Kano da ta dauki matakan kariya ga Kananan Yara don gudun kara afkuwar abin da ya faru da yarinyar nan Haneefa Abubakar da malaminta ya yiwa kisan gilla a nan Kano.
Uwar gidan shugaban kasa ta bayyana hakan ne lokacin da ta je Gidansu Iyayen Hanifa Abubakar domin yi musu ta’aziyyar Rashin ta.
Aisha Buhari ta yabawa Gwamnatin Jihar Kano bisa matakan data dauka tun faruwar lamarin, Sannan ta ce saurin yanke hukunci ga Waɗanda aka Samu da Wannan laifi zai kwantar da hankalin iyaye musamman mata.
Gwamna Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya jaddadawa al’ummar Kano cewa gwamnatin Kano ba za ta kara ko minti guda ba wajen sanya hannu, Idan Kotu ta yanke hukuncin kisa akan Waɗanda ake Zargi.Uwar gidan Shugaban Kasar ta Ziyarci Fadar Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero domin yi Masa ta’aziyyar rashe-rashen da akai a Kano a yan watannin baya.

Murtala Sule Garo yafi kowa Cancantar Zama Mataimakin Gwamnan Kano.
Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta sanar da rufe karɓar biyan kuɗin Hajji na shekarar 2026.
TARON KOYAR DA KIWON KAJI DA KIFI: KPA
Dalung yayi Alhinin halin da Nigeria ke Ciki .
Manoma sun Kira ga Gwamnati Tarayya tayi taka Tsan-Tsan
Gwamna Peter Mbah na Enugu ya koma jam’iyyar APC
Katsina is Investing Resources to Drive Agriculture Development – governor Radda Tells IsDB Delegation
Over 50 Feared Dead in Suspected Military Airstrike at Borno–Yobe Border Market
After Intense Meetings: Kano APC Stakeholders Nominate Sule Garo As Deputy Governor
APC Legacy Stakeholders Submit Deputy Governorship Nominees to Gov. Yusif
Yusuf Disburses N50,000 Monthly Support to 6,680 Women Across Kano
NSCDC Kano Command Tests Surveillance Drone to Boost Security Operations