Menu

Kungiyar ASUU Ta Shiga Yajin Aiki Na Gargadi

Admin 4 years ago

Ƙungiyar malaman jami’a a Najeriya ta Academic Staff Union of Universities (ASUU) ta ayyana shiga yajin aiki na sati huɗu a matsayin gargaɗi ga gwamnatin tarayyar ƙasar.

Shugaban ASUU Farfesa Emmanuel Victor Osodeke ne ya bayyana hakan yayin wani taron manema labarai a yau Litinin bayan wata ganawa da majalisar zartarwar ƙungiyar ta yi ta tsawon kwana biyu.

Samar da ingataccen iImi ne hanyar kawo karshen matsalar rashin tsaro –

Shugaban ƙungiyar reshen Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Wudil, Kano ya ce shugabannin ƙungiyar na jihohoi na kan hanyarsu ta komawa don sanar da ƙungiyoyin nasu halin da ake ciki.