Menu

Zamu kara inganta alakar aiki tsakanin NIMASA da Makarantar kimiyya da fasaha da lamuran sufurin jiragen ruwa – Dr Bashir Jamoh

Admin 4 years ago

Darakta Janar na Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Ruwa ta Najeriya (NIMASA) Dr. Bashir Jamoh yasha alwashin kara inganta alakar aiki tsakanin hukumar da Makarantar kimiyya da fasaha da lamuran jiragen ruwa na Arab Academy for Science, Technology and maritallme Transport dake kasar masar.

Dr Bashir Jamoh ya bayyana hakan ne lokacin da yake karbar mataimakin shugaban makarantar farfesa Alsnosy Mohamed Balbaa, a ofishinsa da ke legas.

Ya kuma gabatar da wani abin tunawa ga Mataimakin Shugaban Makarantar kimiyya da fasaha da lamuran sufurin jiragen ruwa na Arab Academy for Science, Technology & Maritime Transport (AASTMT) dake Masar, mai lura da nahiyoyin Afirka da Asiya, Farfesa Alsnosy Mohamed Balbaa, yayin wani taro da AASTMT kan bunkasa iya aiki a hedkwatar NIMASA da ke Legas, Najeriya.