Menu

Ramadan : Gidan Man Salbas zai sayar da mai tsahon awa 24

Admin 4 years ago

Daga Mukhtar Khalil

Mamallakin Rukunonin Kamfanin Salbas oil and gas Alhaji Sale Baba Rano, ya kudirci aniyar sayar da man fetur ba dare ba Rana har na tsahon kwanaki 7 Albarkacin Wannan wata na Ramadana Mai albarka.

Alhaji Sale Baba Rano ya bayyana hakan ne yayin wata ganawa da yayi da Jaridar Kadaura24 a Yau labaraba .

Salbas yace ya dau wannan matakin ne, domin taimakawa al’umma su samin man a cikin yanayi Mai Sauki a kowanne lokaci Albarkacin watan Azumin Ramadan.

Haka zalika wannan mataki zai taimakawa yunkurin Kamfanin Samar da albarka man fetur na Kasa NNPC, wajen magance karancin man fetur a jihar Kano da kasa baki daya.

” Mun yi Haka ne don saukakawa al’umma, kuma Idan ka lura ana Azumin cikin rana kuma ga wahalar da man yake yi, to Amma Idan muka bada wannan Gudunmawa ta bayar da man awa 24 Ina da tabbacin al’umma zasu sami sauki”.

Salbas yace za’a bayar da man ne a Gidan Man Salbas dake kan titin BUK kusa da Kofar fanfo a birni kano a gobe alhamis 07-04-22, Inda yace an yi tanadi Jami’an tsaro domin tabbatar da cewa an sami ingantaccen tsaron, yayin da ake bayar da man safe Rana da dare har na tsahon kwanaki 7.

Gidan Man dai Yana da kawuna Masu yawa Kuma akwai abubuwan more rayuwa a ciki, don tabbatar da duk Wanda ya je shan man Zai Sha ba tare da wata matsala.

Idan za’a iya tunawa Kadaura24 ta rawaito an jima ana wahalar man fetur a kasar nan, Kuma da alama da Sauran Masu gidajen Mai zasu yi koyi da Alhaji Sale Baba Rano (Salbas) da al’umma sun sami saukin wahalar man da ta Dade tana ciwa al’umma tuwo a kwarya