Menu

Na fita Daga Jam’iyyar APC, Ba’a Yiwa ‘Yan Kano Ta Kudu Adalci ba – Kabiru Alhassan Rurum

Admin 4 years ago

Tsohon Shugaban majalisar dokokin jihar Kano Alhaji Kabiru Alhassan Rurum wanda shine dan majalisa mai wakiltar kana nan hukumomin Rano, kibiya da Bunkure a majalisar wakilai yace ya fice daga jam’ityar APC.

Kabiru Alhassan Rurum ya bayyana hakan ne lokacin da yake zantawa da manema labarai a kano.

” na fice daga jamiyyar ce sakamakon rashin Adalcin da ake yiwa alummar Kano ta Kudu duk da yawan alummar da ke wannan yanki”

Kabiru Alhassan Rurum yace ya fita ne bisa raayin raayin kansa, kuma nan ba da dadewa ba zai sanar da

Jamiyyar da zai koma.

“maganar neman takarar gwanma ta tana nan ba gudu Baja da baya.”

bayanan bayan fage na nuni da cewar ya fice ne sakamakon shirin da akeyi a jamiyyar APC a Kano na tsayar da mataimakin gwamna Dr Nasir yusif Gawuna a matsayin dan takarar gwamna,inda murtala sule Garo zai tsaya mataimakin gwamna.