Menu

Jam’iyyar ADP mai alamar littafi ta tsayar da Alhaji Ibrahim Sabo Sulaiman a matsayin dan takarar gwamnan jihar Jigawa

Admin 4 years ago

2023: Jam’iyyar ADP mai alamar littafi ta tsayar da Alhaji Ibrahim Sulaiman Sabo, a matsayin ɗan takarar gwamna a jihar Jigawa.

Wannan ya biyo bayan tsarin masalaha da jam’iyyar tabi wajen zaben, inda delegate 16 suka amince.

Kafin wannan, sai da jam’iyyar ta zabi yan takarar majalisun jiha da tarayya, wanda shima tsarin masalaha aka bi.

Alhaji Ibrahim Sulaiman Sabo wanda gogaggen dan siyaysa ne wanda ke da kwarewa a fannin harkokin yau da kullum ya sha Alwashin kara bunkasa cigaban jihar muddin alummar jihar suka sahale masa ya zama gwamnan jihar.

alumma da dama da suka zanta da jaridar time express bisa tsayar da Alhaji Ibrahim Sulaiman Sabo da jam’iyyar ADP Mai alamar littafi ta yi a matsatun dan takarar gwamnan jihar jigawa sunce babu shakka shi ne zai lashe zaben gwamnan jihar ta jigawa a kakar zabe Mai zuwa, musamman idan aka yi da irin dumbin masoyan da jam’iyyar ke da shi a jihar jigawan da ma sauran jihohin nigeria