Daga Abdullahi Kano
Dan takarar Sanatan Kano ta kudu a jam’iyyar NNPP Hon. Sulaiman Abdulrahman Kawu Sumaila yace katin zabe shi ne dama ta karshe da talaka zai amfani da ita don zabar shugabanni na gari a Nigeria.
Hon. Kawu Sumaila ya bayyana hakan ne yayin wani tattaki na wayar da kan al’ummar jihar kano don fita su karbi katin zabe da a yanzu haka hukumar zabe ke yi.
Yace akwai matsaloli Masu tarin yawa da suka addabi al’ummar jihar kano da kasa baki daya, wanda kuma talakawa ba za su iya maganinsu ba sai ta hanyar zabar shugabanni nagari, kuma hakan bazai yiwuba sai da katin zabe.
“Shugabanni nagari ne kadai zasu kawo wa al’umma sauki ta fuskar samar da shugabanci nagari, samar da ingantattun dokoki, ingantaccen Ilimi,kiwon lafiya da sauran abubuwan more rayuwa da inganta rayuwar al’umma”.Inji Kawu Sumaila
Dan takarar Sanatan na Kano ta kudu ya ce mata da matasa su ne abun tausayi yanzu a Nigeria saboda su ne suka fi yawa a cikin al’umma, kuma su ne suka rasa abubuwan more rayuwa wadanda ya kamata ace suna da shi, don haka ya bukace su da su mai da hankali wajen ganin sun je sun yanki katin zabe don su zabi wadanda zasu inganta rayuwar su.
“Wajibi ne mata su fito su karbi katin zabe saboda da su ne suke zuwa asibiti domin haihuwa ko su kai yaransu to sun san halin da suke ganin asibitocinmu, kuma ya’yansu ne suke zaune ba aikin yi , da dai sauran matsaloli da dole sai sun bada gudunmawar su ta hanyar yin katin zabe domin zabar shugabanni nagari”. Inji Kawu Sumaila
Hon. Kawu Sumaila da Abba Kabir Yusuf dan takarar gwamnan jihar Kano a NNPP da sauran jiga-jigan jam’iyyar na daga cikin wadanda suka fito tattakin, wanda aka fara daga gidan Engr. Rabi’u Musa Kwankwaso dake Miller Road a nan Kano.

Murtala Sule Garo yafi kowa Cancantar Zama Mataimakin Gwamnan Kano.
Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta sanar da rufe karɓar biyan kuɗin Hajji na shekarar 2026.
TARON KOYAR DA KIWON KAJI DA KIFI: KPA
Dalung yayi Alhinin halin da Nigeria ke Ciki .
Manoma sun Kira ga Gwamnati Tarayya tayi taka Tsan-Tsan
Gwamna Peter Mbah na Enugu ya koma jam’iyyar APC
Bichi Moves Motion as Kano APC Stakeholders Endorse Tinubu for 2027, Raise N50m for Nomination Form
Yusuf Orders Probe into Alleged N1.5bn Salary Deductions in Kanoi
Fred Itua named Group Politics Editor, The Sun Newspaper
Sharada Joins Kano Central Senatorial Race, Calls for Free and Fair APC Primaries
NEPC trains SMEs, MSMEs in Kano to boost export readiness
Traditional institutions key to security, peace building in Nigeria, security – CAS