Hukumar kula da iyakokin ruwa ta kasa-NIMASA ta sanya hannun a yarjejeniyar fahimtar juna da cibiyar kula da harkokin sufuri ta kasa-NITT ta fuskar bincike da horaswa don inganta tsaro akan iyakokin ruwan kasar nan.
Shugaban hukumar NIMASA, Dr Bashir Jamoh da takwaransa na NITT ne suka sa hannun da zimmar inganta kayayyakin da ake kerawa na cikin gida.
Ita da wannan yarjejeniya ta fahimta a wani bangare na nuna burin da hukumomin biyu ke da shi ne wajen ganin manyan ma’aikata a bangaren sha’anin iyakokin ruwa na samun horo na musamman a nan gida Nijeriya ba sai sun tsallaka kasashen ketare ba.
Dr Bashir Jamoh ya bayyana yarjejeniyar fahimtar junan a matsayin wacce ta ke da nufin cika babbar manufar kafa cibiyar kula da harkokin sufuri ta kasa, da kuma jaddada kudirin da hukumar NIMASA ke da shi na horas da ma’aikatan ta.
Ya kuma bayyana fatan cewa yarjejeniyar zata kyautata alaqa a tsakanin hukumomin, sannan ya bukaci cibiyar da ta cigaba da gudanar da bincike mai zurfi don bunkasa horaswa.
A nashi bangaren, Shugaban cibiyar kula da harkokin sufuri ta kasa, Dr Bayero Salih Farah ya bayyana godiyar shine ga hukumar NIMASA bisa ga gudunmawar da take baiwa cibiyar ta fuskar tallafin kudi na kai tsaye da kuma bada daman horas da ma’aikatan ta NIMASA shekara da shekaru.
Ya kuma sha alwashin cewa cibiyar za tayi aiki tare da NIMASA da kuma tabbatar da cewa cibiyar tana bada horaswa da gudanar da bincike-bincike daidai da na zamani.
Dr Bayero Salih Farah yace cibiyar na horas da ma’aikata da ke aiki a bangaren sufuri inda take bada shaidar takardun diploma, babbar diploma, da ta shaidar digiri na biyu a sha’anin sufuri.
A daya bangaren kuma NIMASA na cigaba da rungumar horas da ma’aikatanta don inganta kula da iyakokin ruwan Nijeriya da kuma hada gwiwa da ma’aikatu da dama don samar da tsaro a kan iyakokin na ruwa.


Murtala Sule Garo yafi kowa Cancantar Zama Mataimakin Gwamnan Kano.
Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta sanar da rufe karɓar biyan kuɗin Hajji na shekarar 2026.
TARON KOYAR DA KIWON KAJI DA KIFI: KPA
Dalung yayi Alhinin halin da Nigeria ke Ciki .
Manoma sun Kira ga Gwamnati Tarayya tayi taka Tsan-Tsan
Gwamna Peter Mbah na Enugu ya koma jam’iyyar APC
Katsina is Investing Resources to Drive Agriculture Development – governor Radda Tells IsDB Delegation
Over 50 Feared Dead in Suspected Military Airstrike at Borno–Yobe Border Market
After Intense Meetings: Kano APC Stakeholders Nominate Sule Garo As Deputy Governor
APC Legacy Stakeholders Submit Deputy Governorship Nominees to Gov. Yusif
Yusuf Disburses N50,000 Monthly Support to 6,680 Women Across Kano
NSCDC Kano Command Tests Surveillance Drone to Boost Security Operations