Menu

Hana shigo da abinci Nigeria babbar Matsala ce – Sarki Mohammadu Sanusi II

Admin 4 years ago

Maimartaba Sarkin Kano na goma sha hudu kuma Khalifan Tijjaniyya a Najeriya ya caccaki matakin gwamnatin Najeriya na hana shigowa da abinci kasar yana mai cewa mataki ne da ba zai haifar wa Najeriya d’a mai ido ba.

Tsohon Sarkin na Kano wanda masanin tattalin arziki ne kuma tsohon gwamnan babban bankin kasa ne “CBN” ya ce hana shigowa da abinci ba zai ta’ba maganin koma bayan tattalin arziki da Najeriya ke fuskanta ba.

Jaridar Daily Post ta ruwaito cewa Tsohon Sarkin ya yi wannan jawabi ne a matsayin bako na musamman a wani taron jama’a da aka gabatar a karshen mako.

“Rashin samar da kayyayakin gida masu muhimmanci shi ne abin da ya kamata a magance tare da canjin manufofin da za su fitar da kasar ga gaci da kuma ci gaba a samar da kayyayaki na gida ba wai dakatar da shigo da abinci ba.” A cewar Tsohon Sarkin Kano Sunusi

Ya kuma bukaci gwamnatin tarayya da ta yanke shawarar tattalin arzikin da take so ta gudanar.

Tun hawan Buhari mulki al’umma ke kokawa da yunwa gami da tsadar rayuwa musamman hauhawar farashi, wanda masana suka ce matakan gwamnatin Buhari ne suka sabbaba. Tuni al’ummar Najeriya suka dora laifin halin da tattalin arzikin da kasar ke ciki a kan gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari, cewa ba su taba riskar irin wannan ba kafin zuwan Buharin.

asalin labari jaridar Rariya