Majalisar wakilai ta Najeriya ta bayyana takaici tare da yin Allah wadai da kashe wata yarinya Ummukulsum Sani Buhari da wani Dan kasar Sin yayi a karshen makon daya gabata..
Majalisar tayi Allah wadai da lamarin ne Sakamakon kudirin gaggawa da Wakilin Kananan hukumomin Rano, Kibiya da Bunkure a majalisar Rt Hon Kabiru Alhassan Rurum yayi inda ya bayyana kisan a matsayin na zalinci Kuma Wanda ya Saba doka.
A yayin Dayake gabatar da kudirin Turakin na Rano ya bukaci majalisar ta yi Kira ga hukumomin tsaro su gudanar da kwakwkwaran bincike su Kuma gurfanar da Wanda ake zargin a gaban kotu Dan ya girbi abinda ya shuka.
Ya Kuma bukaci ‘Yan majalisar dasu tashi tsayi ayi shiru na Minti daya da zummar yin Addua ga marigayiyar tare da bukatar a kafa kwamitin da zai ziyarci Jihar Kanon da lamarin ya faru Dan jajantawa iyaye da ‘yan uwan Yarinyar dama Gwamnatin jihar baki daya..
Kudirin dai ya samu cikakken goyon baya ga daukacin ‘yan majalisar da suka halacci zaman in Banda wani Dan majalisar dake wakiltar wata mazaba a cikin Birnin Kano Wanda ya nuna rashin goyon bayansa tare da cewar Bai maga dalilin kawo wannan KUDIRI ba.
Tuni dai kudirin ya samu karbuwa Kuma majalisar ta amince da bukatu da Wakilin Kananan hukumomin na Rano, Kibiya da Bunkure Rt Hon Kabiru Alhassan Rurum ya gabatar cikin kudirin nasa…
A ranar Asabar data gabata ne dai wani Dan kasar China mazaunin Jihar Kano Geng Quarong ya haura har gidan su wata yarinya Budurwarsa Ummita dake Unguwar Jan bulo ya caccaka mata Wuka har ta mutu sakamakon kin karbar bukatar autensa da tayi..
Fatihu Yusuf Bichi
22/8/2022

Murtala Sule Garo yafi kowa Cancantar Zama Mataimakin Gwamnan Kano.
Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta sanar da rufe karɓar biyan kuɗin Hajji na shekarar 2026.
TARON KOYAR DA KIWON KAJI DA KIFI: KPA
Dalung yayi Alhinin halin da Nigeria ke Ciki .
Manoma sun Kira ga Gwamnati Tarayya tayi taka Tsan-Tsan
Gwamna Peter Mbah na Enugu ya koma jam’iyyar APC
Katsina is Investing Resources to Drive Agriculture Development – governor Radda Tells IsDB Delegation
Over 50 Feared Dead in Suspected Military Airstrike at Borno–Yobe Border Market
After Intense Meetings: Kano APC Stakeholders Nominate Sule Garo As Deputy Governor
APC Legacy Stakeholders Submit Deputy Governorship Nominees to Gov. Yusif
Yusuf Disburses N50,000 Monthly Support to 6,680 Women Across Kano
NSCDC Kano Command Tests Surveillance Drone to Boost Security Operations