Babban Sakataren hukumar kula da iyakokin ruwa na duniya, Mr Kitack Lim zai ziyarci Nijeriya daga ranar ashirin zuwa ashirin da biyu na wannan wata don halartar taron karawa juna sani a bangaren iyakokin ruwa.
A sanarwar da mataimakin darakta a sashin hulda da jama’a na hukumar NIMASA Mr Edward Osagie ya fitar ya ce ma’aikatar sufuri da hukumomin dake karkashinta ne suka shirya taron.
A cewar Ministan Sufuri, Injiniya Mu’azu Sambo yace a shirye gwamnatin tarayya take wajen samar da kyakkyawar yanayi ga masu ruwa da tsaki a bangaren iyakokin ruwa don cimma manufar da aka sanya a gaba.
A nashi tsokacin, Shugaban hukumar kula da iyakokin ruwan kasar nan, Dr Bashir Yusuf Jamoh yace wannan ziyara ta Mr Kitack Lim wanda itace karo na farko a shekaru goma sha biyar da suka gabata, wata manuniya ce dake nuna karbuwar Nijeriya a idon duniya.
Yayi nuni da cewa Nijeriya zata cigaba da inganta bangarenta na iyakokin ruwa har sai ta shiga sahu na farko a fadin duniya.
A cewar Mr Emeka Akabogu, taron na karawa juna sani wata dama ce ta tattauna batutuwan da suka shafi bangaren a aikace da nufin samar da hanyoyin magance kalubalen dake fuskantar bangaren.
Ana sa ran Mr Kitack Lim zai ziyarci hukumar NIMASA don ganewa idon shi yanda take gudanar da ayyukanta kasancewar ta itace hukuma daya tilo a karkashin ma’aikatar sufuri dake da alaqa da hukumar kula da iyakokin ruwa na duniya.

Murtala Sule Garo yafi kowa Cancantar Zama Mataimakin Gwamnan Kano.
Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta sanar da rufe karɓar biyan kuɗin Hajji na shekarar 2026.
TARON KOYAR DA KIWON KAJI DA KIFI: KPA
Dalung yayi Alhinin halin da Nigeria ke Ciki .
Manoma sun Kira ga Gwamnati Tarayya tayi taka Tsan-Tsan
Gwamna Peter Mbah na Enugu ya koma jam’iyyar APC
Bichi Moves Motion as Kano APC Stakeholders Endorse Tinubu for 2027, Raise N50m for Nomination Form
Yusuf Orders Probe into Alleged N1.5bn Salary Deductions in Kanoi
Fred Itua named Group Politics Editor, The Sun Newspaper
Sharada Joins Kano Central Senatorial Race, Calls for Free and Fair APC Primaries
NEPC trains SMEs, MSMEs in Kano to boost export readiness
Traditional institutions key to security, peace building in Nigeria, security – CAS