Menu

Dalung yayi Alhinin halin da Nigeria ke Ciki .

Admin 4 months ago
Usman Ahmed, kaduna
Barrister Solomon Dalung, tsohon ministan matasa da wasanni zamanin marigayi Shugaba Muhammadu Buhari, yayi tsokaci a yayin zantawa da yan jarida lokacin gudanar da bikin cika shekaru ashirin da biyar da kafuwar kungiyar Dattawan Arewa.
A fadinsa, tsohon ministan  yace  kamata yayi ace Kuka a keyi da alhini, ba bikiba.
Yace “yaran mu fiye da dari, Mata, yan makaranta na tare da yan bindiga a daji, wadanda aka daukesu karfi da yaji a makarantunsu.
Ya Kara da cewa kamata yayi a yi alhini, ayi dubi, ta duk yadda za’a kubutar da kananan yan makarantar, Wanda basu ji ba, Basu gani ba.
Yace, yanzu haka iliminsu ya zama wani abu, la’akari da halin dasu ke ciki.
Ya Kara da cewa, “yanzu da ace yaranmu na cikinsu, da bama nan, dole muna chan, nemar mafitarsu”.
Ya Kuma ce, ya zama dole a samar musu mafita.
Akarshe ya yabawa kungiyar Dattawan Arewa da nasu kokarin na gudanar da taron, da Kuma Kira ga al’ummar Arewa dasu kula da ilimi, noma da kasuwanci