Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, ya ba da umarnin a dauki sabbin ‘yan sanda dubu 10,000 a kasar.
Mai taimakawa Buhari a fannin yada labarai ta kafafen zamani Bashir Ahmad ne ya bayyana hakan cikin wani sako da ya wallafa.
“Shugaba Muhammadu Buhari ya ba da umarnin a dauki ‘yan sanda 10,000 a matsayin jami’an ‘yan sanda a jihohi 36 da babban birnin tarayyar Abuja.” Ahmad ya ce.
An dauki wannan mataki ne, “don a tunkari kalubalen tsaro a wasu sassan kasar.”
A cewar sanarwar, an dauki mutum 10 ne a kowace karamar hukuma cikin kananan hukumomi 774 da ke Najeriya, kuma tuni har an sanar da wadanda aka dauka ta hanyar emel da suka nemi aikin.
Daukan karin ‘yan sanda a aiki na zuwa ne yayin da Najeriya ke fuskantar matsalolin tsaro a sassanta.
A Arewa maso yammacin kasar na fama da ‘yan fashin daji da ke kai hare-hare da sace mutane domin neman kudin fansa.
Arewa maso gabashi kuma tana fama da matsalar Boko Haram da ISWAP, yayin da a kudu maso gabashin kasar take fama da matsalar ‘yan awaren kungiyar IPOB.

Murtala Sule Garo yafi kowa Cancantar Zama Mataimakin Gwamnan Kano.
Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta sanar da rufe karɓar biyan kuɗin Hajji na shekarar 2026.
TARON KOYAR DA KIWON KAJI DA KIFI: KPA
Dalung yayi Alhinin halin da Nigeria ke Ciki .
Manoma sun Kira ga Gwamnati Tarayya tayi taka Tsan-Tsan
Gwamna Peter Mbah na Enugu ya koma jam’iyyar APC
Bichi Moves Motion as Kano APC Stakeholders Endorse Tinubu for 2027, Raise N50m for Nomination Form
Yusuf Orders Probe into Alleged N1.5bn Salary Deductions in Kanoi
Fred Itua named Group Politics Editor, The Sun Newspaper
Sharada Joins Kano Central Senatorial Race, Calls for Free and Fair APC Primaries
NEPC trains SMEs, MSMEs in Kano to boost export readiness
Traditional institutions key to security, peace building in Nigeria, security – CAS