Menu

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta sanar da rufe karɓar biyan kuɗin Hajji na shekarar 2026. 

Admin 4 months ago

Darakta Janar na Hukumar, Alhaji Lamin Rabi’u Danbappa, ya bayyana cewa wa’adin karɓar kuɗaɗen ya ƙare ne a ranar Juma’a, 5 ga Disamba, 2025.

Ya ce, bayan kammala taro da Hukumar Alhazai ta Ƙasa (NAHCON) an Abuja ranar Alhamis da ta gabata, ba a samu ƙarin wa’adi ba wajen karɓar kuɗin.

Alhaji Lamin Rabi’u Danbappa ya bayyana hakan ne yayin taron da ya gudanar da dukkan masu ruwa da tsaki a Hukumar.

Ya yi bayanin cewa rufe karɓar kuɗin da wuri ya zama dole ne sakamakon sabbin ƙa’idoji da dokoki da hukumomin Saudiyya suka gabatar domin gudanar da aikin Hajjin 2026.

Sabbin ƙa’idojin sun tanadi tsauraran matakai da bukatar kammala shirye-shiryen gudanar da aikin Hajji tun da wuri, domin tabbatar da tafiyar da al’amura yadda ya kamata ga masu niyyar zuwa.