Shugaban hukumar kula da iyakokin ruwan kasar nan, Dr Bashir Yusuf Jamoh ya sadaukar da lambar girmamawar da Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bashi ga masu ruwa da tsaki a bangaren iyakokin ruwan kasar bisa namijin kokarin da suke yi wajen ciyar da bangaren gaba.
A sanarwar da mataimakin darakta a sashin hulda da jama’a na hukumar, Mr Edward Osagie ya rabawa manema labarai a birnin Ikko, yace Dr Bashir Yusuf Fagge ya bayyana hakan ne jim kadan bayan karban lambar girmamawar wanda aka yi a wannan mako a babban birnin tarayya, Abuja.
Dr Bashir Yusuf Jamoh ya kuma yabawa Ministan harkokin sufuri, Mu’azu Jaji Sambo da hukumar gudanarwar NIMASA dangane tsayin dakar da suke yi wajen habbaka bangaren iyakokin ruwan kasar nan, sannar ya sha alwashin kara bada himma sauke nauyin dake wuyan shi.
Shugaban hukumar har ila yau ya mika godiyar shi ga dukkan wadanda suka taya shi farin ciki bisa wannan wannan lambar girmamawa ta kasa da ya samu, inda ya ce wannan zai zaburar da shi wajen cigaba da yiwa kasa hidima.
A nashi bangaren, Ministan harkokin sufuri, Mu’azu Jaji Sambo yace babu shakka, Dr Bashir Jamoh ya cancanci samun wannan lambar girmamawa ta kasa dangane da sauye-sauyen da ya kawo tun bayan nada shi a matsayin Shugaban hukumar NIMASA da kuma kokarin shi wajen kare iyakokin ruwan kasar nan daga ayyukan mabarnata.
A nashi tsokacin, tsohon shugaban hukumar NIMASA, Dr Ade Dosunmu ya yaba da jajircewar Dr Bashir Jamoh ne wajen gudanar da aiki, sannan yace tabbas ya cancanta da samun wannan yabon girma.
Shi kuwa Sanata Danjuma La’ah yace jihar Kaduna da Al’ummar ta na alfahari da Dr Bashir Yusuf Jamoh.

Murtala Sule Garo yafi kowa Cancantar Zama Mataimakin Gwamnan Kano.
Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta sanar da rufe karɓar biyan kuɗin Hajji na shekarar 2026.
TARON KOYAR DA KIWON KAJI DA KIFI: KPA
Dalung yayi Alhinin halin da Nigeria ke Ciki .
Manoma sun Kira ga Gwamnati Tarayya tayi taka Tsan-Tsan
Gwamna Peter Mbah na Enugu ya koma jam’iyyar APC
Bichi Moves Motion as Kano APC Stakeholders Endorse Tinubu for 2027, Raise N50m for Nomination Form
Yusuf Orders Probe into Alleged N1.5bn Salary Deductions in Kanoi
Fred Itua named Group Politics Editor, The Sun Newspaper
Sharada Joins Kano Central Senatorial Race, Calls for Free and Fair APC Primaries
NEPC trains SMEs, MSMEs in Kano to boost export readiness
Traditional institutions key to security, peace building in Nigeria, security – CAS