Menu

Zaben 2023: Alummar Nigeria za su Dara in Muka Sami Dama – Jam’iyyar PRP

Admin 4 years ago

Daga Abdullahi Kano

Jamiyyar PRP tace muddin alummar kasar nan su ka ba ta dama ta hanyar zaben ‘ya ‘yanta a mukamai daban daban a shekara ta 2023 to babu shakka zasu sami canji na gaske,wanda zai kai kasar nan tudun mun tsira.
Shugaban jam’iyyar reshen jihar kano Alhaji Abba Sule Namatazu ne ya bayyana hakan yayin wani taro da jam’iyyar ta gudanar a dakin taro na cibiyar nazarin harkokin demokraddiya da ke gidan Mumbayya a kano.
Alhaji Abba sule Namatazu yace jam’iyyar na kan thatttaunawa da ‘yayanta a dukkan sassan kasar nan don farfado da ita,da kuma stara yadda zaa tunkari zabe mai zuwa don lashe dukkanin zabubbukan da ke tafe.

Shugaban jamiyyar yana Mai cewar jamiyyar PRP jam’iyya ce Mai tsantseni da son talakawa, don haka muddin suka sami damar Jan ragamar alumma a kowani mataki to baby shakka alummar kasar nan za us Dara.
Yayi fatan tan jam’iyyar zasu jajirce tare da kara sadaukar da Kai wajen cimma nasarorin da aka sanya a gaba.
A nasa jawabin mai rimon mukamin sakataren jam’iyyar ta kasa malam Kabiru Mohammad Gwangwazo yace lokaci yayi da alummar kasar nan zasu canji na gaskiya, wanda talaka zai gani a kasa musamman ta fuskar inganta tsaro,magance matsalar hauhawar farashin kayan masarufi da tsadar rayuwa wacce ta je fa talaka colon halin kaka nikayi.
Da yake jawabi tun farko kakakin jam’iyyar a kano Alhaji Musa Maigari yace makasudin taron tattaunawar shi ne don a lalubo bakin zaren don ciyar da kasa gaba.
Bisa haka ne ya bukaci alummar jihad kano da na kasa baki daya da suyi fitar farar dango don shiga jam’iyyar ta PRP, inda yace itace jirgin fiton talakawa daga halin da suke ciki.
Taron ya sami halartar shugabbanin jam’iyyar na jihohi, sauran ‘yan jam’iyya da masu ruwa da tsaki.