Menu

Yan jam’Iyyar APC muyi Hakuri mu zauna lafiya -Kunigiyar We#standwith Danzago

Admin 4 years ago

Sabuwar Kungiyar magoya bayan jam’iyyar APC mai suna we#standwith Danzago ta bayyana a jihar kano.

bayanin hakan na dauke a wata takarda wacce jami’in hulda da jamaa na kungiyar Mukhtar Gwammaja ya sanyawa hannu aka Arakawa manema labarai a kano

Ga jawabin Jagoran kungiyar Barrister Abdulziz “Tare da sallama irin ta addinin musulunci, da fatan alkhairi ga alumar jihar Kano musamman magoya bayan jamiyyar APC Muna Mai gabatar  da wannan sabuwar tafiya Mai suna We#standwith Danzago Dan ci gaban jamiyyar  APC a jihar kano da kasa baki daya.”
“Wannan kungiya na Kuma Kara  jaddada goyon bayan ta ga Mai girma Ambassador Amadu Haruna Zago. Tana Kuma Kira ga daukacin yayan jamiyyar APC da su Yi hakuri su zauna a jamiyyar APC Dan ci gaban kasa.”

 Yace daga cikin manufofin kungiyar sun hada da

1.  tallata manufofin jamiyyar APC a jihar kano  Dan samun nasara zabubbukan 2023

2.kare martaba da mutunci na Mai girma Ambassador Amadu Haruna Zago.

3. Tuntuba da ziyarar Yan jamiyyar APC a kanaanan hakumomi arbain da gudu Dan wayar da kansu a zabi jamiyyar APC a jihar kano.

4. Gabatar da tarruruka a unguwanni Dan samun nasrar jamiyyar APC a jihar kano.

Shugabannin kungiyar su ne

Chairman barrister Abdulaziz
Deputy chairman Hajiya Amina kamilu
Secretary Dr Abdulkadir Ahmad JoganaAssistant secretary Mohd yakubu Danhassa
Organizing secretary Hussain Dan mukulli
Directory press  Mukhtar B.A.A Gwammaja 
Treasurer  muhammad uba sukilala
Women leader Hajiya Aisha Ibrahim
Youths leader Dr Suleiman isyaku
Legal adviser Barrister Rabiu saidu
Auditor  miftahu ishaq