Menu

Zamu gina titin da ya tashi daga gidan masu lalurar kwakwalwa na yamadawa Dorayi zuwa Tunga – Hon Abdullahi Lawan Kenken

Admin 4 years ago

Dan majalisa mai wakiltar karamar hukumar Gwale Hon Abdullahi Lawan kenken ya alkawari malala kwalta daga gidan masu larurar kwakwalwa na Yamadawa Dorayi wanda yabi ta Tunga har zuwa iyakar Gwale da karamar hukumar Kumbotso .

 Alh Lawan kenken ya bayyana haka ne yayinda yake kaddamar da aikin titi a unguwar sani mainagge da ke Kano.

yace wannan hanya tana cikin hanyoyin da suke ci masa tuwo a kwarya , ya kara da cewa yasha bada gudunmawa ana zuba kasa ana yin ciko a wannan hanya, don haka da izinin Allah za ayi wannan titi nan bada dadewa ba.

Yana Mai cewar maaikatar kula da zaizayar kasa ce zata gudanar da wannan aiki.