Daga Sani Danbala Gwarzo
Shugaban kungiyar malaman makarantun Sakandire na kasa reshen jihar Kano Kwamared Abdu Usman Yalo ya bayyana cewa kasar nan na fatan samun Shugaban da zai bada kulawa sosai a sha,anin Ilmi.
Ya bayyana haka ne lokacin da yake ganawa da manema labarai a ofishinsa yace babu shakka harkar Ilimi abu ne da yakamata shuwagabanni su bawa fifiko fiye da sauran ayyuka.
Ya kara da cewa Gwamnatin kano tayi kokari wajen inganta sha,anin Ilmi musamman tsarin maida Ilimi kyauta kuma dole da kuma samar da kayayyakin koyo da koyarwa a makarantu gami da gyara gine ginen makarantu a fadin jihar.
Kwamared Yalo yace a Shugabancinsa na wannan kungiya sun cimma nasarori da dama ciki harda Samawa malamai lamuni a bankin Samar da muhalli ga al,umma wato (Federal Mortgage Bank) a inda tuni shiri yayi nisa na Samawa malamai 500 lamuni a Bankin a kashi na farko.
Ya kara da cewa baya ga haka akwai tsari na samar da Babura lamuni wanda shima malamai da dama zasu amfana a inda shima shiri yayi nisa wajen rabon baburan.
Abdu Usman Yalo yayi kira ga malaman da su cigaba da jajurcewa wajen sauke nauyin da ya rataya a wuyansu don cigaban Ilimi a fadin jihar kano dama kasa baki daya.

Murtala Sule Garo yafi kowa Cancantar Zama Mataimakin Gwamnan Kano.
Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta sanar da rufe karɓar biyan kuɗin Hajji na shekarar 2026.
TARON KOYAR DA KIWON KAJI DA KIFI: KPA
Dalung yayi Alhinin halin da Nigeria ke Ciki .
Manoma sun Kira ga Gwamnati Tarayya tayi taka Tsan-Tsan
Gwamna Peter Mbah na Enugu ya koma jam’iyyar APC
Governor Radda Distributes Subsidized Fertiliser across 6,652 Pollint Units
Police Order Joint Operations After Pirate Attack on Calabar–Oron Waterway
FG Intensifies Oversight of Kano–Zaria–Kaduna Rail Project
Shekarau Defect to APC After Consultations
Dropping Rurum for Deputy Governor: Gamble Gov Yusuf Cannot Afford – Analyst Warns